< Psalms 33 >

1 Be joyful, O ye righteous, in the Lord; [for] unto the righteous praise is comely.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Give thanks unto the Lord with the harp: with the ten-stringed psaltery do ye sing [praises] unto him.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Sing unto him a new song; play beautifully amidst a triumphant shout.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 For the word of the Lord is upright; and all his works [are done] in truth.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 He loveth righteousness and justice: the earth is full of the kindness of the Lord.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 By the word of the Lord were the heavens made; and by the breath of his mouth all their host.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 He gathereth together like heaps the waters of the sea: he layeth up in store-houses the depths [of the sea].
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Let all the earth fear the Lord: of him stand in awe all the inhabitants of the world.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 For he spoke, and it came into being: he commanded, and it stood fast.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 The Lord frustrateth the resolves of the nations: he bringeth to nought the thoughts of the people.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 The counsel of the Lord will stand for ever, the thoughts of his heart from generation to generation.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Happy is the nation whose God is the Lord, the people whom he hath chosen for himself as a heritage.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 The Lord looketh from heaven; he seeth all the sons of men.
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 From the place of his habitation he directeth his view upon all the inhabitants of the earth;
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 He fashioneth their hearts altogether; he hath regard to all their works.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 The king is not saved by the multitude of an army: a mighty man is not delivered by much strength.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Vain is the horse for victory: nor shall he deliver any by the greatness of his strength.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Behold, the eye of the Lord is upon those that fear him, upon those that hope for his kindness.
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 To deliver from death their soul, and to keep them alive in famine.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Our soul waiteth for the Lord: our help and our shield is he.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 For in him shall our heart rejoice: because in his holy name have we trusted.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Let thy kindness, O Lord, be upon us, even as we hope in thee.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Psalms 33 >