< Psalms 26 >
1 “Of David.” Judge me, O Lord; for I have indeed walked in my integrity: and in the Lord have I trusted; I shall not slip.
Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
2 Try me, O Lord, and prove me; purify my reins and my heart.
Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
3 For thy kindness is before my eyes; and I have walked in thy truth.
gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
4 I have not sat with men of falsehood, and with dissemblers will I not enter [in communion].
Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
5 I have hated the assemblage of evil-doers; and with the wicked will I not sit.
na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
6 I will wash in innocency my hands, and I will compass thy altar, O Lord:
Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
7 That I may publish with a loud voice [my] thanksgiving, and relate all thy wondrous deeds.
ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 Lord, I love the site of thy house, and the place where thy glory dwelleth.
Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
9 Take not away with sinners my soul, nor with men of blood my life;
Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
10 In whose hands are wicked devices, and whose right hand is full of bribes.
waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
11 But as for me, I will walk in my integrity: redeem me, and be gracious unto me.
Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
12 My foot standeth on an even place: in assemblies will I bless the Lord.
Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.