< Psalms 17 >
1 “A prayer of David.” Hear, O Lord, [the cause of] righteousness, attend unto my entreaty, give ear unto my prayer, coming from lips without deceit.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 Let from thy presence my sentence come forth; let thy eyes behold what is right.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Thou hast proved my heart; thou hast thought of me in the night; thou hast refined me—thou couldst find nothing: my purpose doth not pass beyond [the words of] my mouth.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 Among the deeds of men did I observe, by the word of thy lips, the paths of the dissolute.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 My steps held firmly to thy tracks, [and] my footsteps did not slip.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 I call on thee, for thou wilt answer me, O God: incline thy ear unto me, hear my speech.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Show marvelously thy loving-kindnesses, O thou that savest those who put their trust [in thee] from those that rise up [against them] by thy right hand.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Keep me as the apple of the eye; conceal me under the shadow of thy wings,
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 From the wicked that despoil me, my enemies, who, to take my life, compass me about.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 They are enclosed in their own fat: with their mouth they speak proudly.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 On our steps they now encompass us: they direct their eyes to turn aside in the land.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 Every man is just like a lion that is greedy to tear his prey, and like a young lion lurking in a covert.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Arise, O Lord, prevent him, cast him down; deliver my soul from the wicked, who is thy sword, —
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 From these men—thy hand—O Lord, from the men of this world, whose portion is in this life, and whose belly thou fillest with thy hidden treasure: they have children in plenty, and leave the rest of their substance to their babes.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 As for me, in righteousness shall I behold thy face: I shall be satisfied, when I awake, with contemplating thy likeness.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.