< Psalms 15 >

1 “A psalm of David.” Lord, who may sojourn in thy tent? who may dwell on thy holy mount?
Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
2 He that walketh uprightly, and worketh righteousness, and speaketh the truth in his heart;
Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
3 That uttereth no calumny with his tongue, that doth no evil to his neighbor, and bringeth no reproach on his fellow-man;
ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
4 In whose eyes the despicable is despised; but that honoreth those who fear the Lord; that sweareth to his own injury, and changeth not;
wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
5 That putteth not out his money for interest, and taketh no bribe against the innocent. He that doth these things shall not be moved to eternity.
wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.

< Psalms 15 >