< Psalms 147 >
1 Hallelujah; for it is good to sing praises unto our God; for it is comely; [him] becometh praise.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 The Lord buildeth up Jerusalem: the outcasts of Israel will he gather together;
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 He that healeth the broken-hearted, and bindeth up their hurts;
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Who counteth the number of the stars; who calleth them all by [their] names.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Great is our Lord, and abundant in power: his understanding is immeasurable.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 The Lord helpeth up the meek: he bringeth down the wicked to the ground.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Lift up a song unto the Lord with thanksgiving; sing praises unto our God with the harp;
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 Who covereth the heaven with clouds, who prepareth rain for the earth, who causeth grass to grow upon the mountains;
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Who giveth to the beast its food, to the young ravens which cry.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Not in the strength of the horse hath he delight: nor in the [swiftness of the] legs of man taketh he pleasure.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 The Lord taketh pleasure in those that fear him, that wait for his kindness.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Glorify, O Jerusalem, the Lord: praise thy God, O Zion.
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 For he hath strengthened the bars of thy gates; he hath blessed thy children in the midst of thee;
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 He who bestoweth peace in thy borders, who satisfieth thee with the best of wheat;
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 He who sendeth forth his decree unto the earth: how swiftly speedeth his word along!
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 He who dispenseth snow like wool; who streweth about the hoarfrost like ashes;
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 He who casteth down his ice like pieces: before his cold who can stand?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 He sendeth out his word, and melteth them: he causeth his wind to blow, and waters run along.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 He declareth his word unto Jacob, his statutes and his ordinances unto Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He hath not done so unto any nation: and [his] ordinances— these they know not. Hallelujah.
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.