< Psalms 143 >

1 “A psalm of David.” O Lord, hear my prayer, give ear to my supplications: in thy faithfulness answer me, in thy righteousness.
Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
2 And enter not into judgment with thy servant; for no living man can be regarded righteous before thee.
Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
3 For the enemy hath pursued my soul; he hath crushed to the ground my life; he hath made me dwell in darkness, as those that are dead eternally.
Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
4 And my spirit within me is overwhelmed: in my bosom is my heart astounded.
Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
5 I remember the days of olden times: I meditate on all thy doings: on the work of thy hands do I reflect.
Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
6 I spread forth my hands unto thee: my soul [longeth] for thee, as a thirsty land. (Selah)
Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
7 Hasten, answer me, O Lord, my spirit falleth: hide not thy face from me, that I may not become like those that go down into the pit.
Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
8 Cause me to hear in the morning thy kindness; for in thee do I trust: cause me to know the way whereon I should walk; for unto thee do I lift up my soul.
Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
9 Deliver me, O Lord, from my enemies: by thee do I seek shelter.
Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
10 Teach me to do thy will; for thou art my God: thy spirit is good; guide me on a level land.
Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
11 For thy sake, O Lord, revive me: in thy righteousness bring forth out of distress my soul.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
12 And in thy kindness destroy my enemies, and annihilate all the adversaries of my soul; far I am thy servant.
A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.

< Psalms 143 >