< Psalms 14 >

1 “To the chief musician, by David.” The worthless fool saith in his heart, There is no God. They are corrupt, they are abominable [in their] doings, there is none that doth good.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
2 The Lord looketh down from heaven upon the children of men, to see if there be one intelligent, one who seeketh for God.
Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 They are all gone aside, they are altogether become corrupt: there is none that doth good, no, not even one.
Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
4 Is there no knowledge in all the workers of wickedness? who eat up my people as they eat bread; [while] they do not call on the Lord.
Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
5 There are they terrified in terror; for God is with the righteous generation:
Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
6 The counsel of the poor [though] you put to shame; because the Lord is his protection.
Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
7 Oh that some one might bring the salvation of Israel out of Zion! When the Lord bringeth back the captivity of his people, then will Jacob be glad, and Israel will rejoice.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!

< Psalms 14 >