< Psalms 116 >

1 It is lovely to me that the Lord heareth my voice, my supplications.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 For he hath inclined his ear unto me: therefore throughout all my days will I call on him.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 The bands of death had compassed me, and the pangs of the nether world had overtaken me; I had met with distress and sorrow: (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
4 I then called on the name of the Lord, I beseech thee, O Lord, release my soul.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 Gracious is the Lord, and righteous; and our God is merciful.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 The Lord preserveth the simple: I was in misery, and he helped me.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Return, O my soul, unto thy rest; for the Lord hath dealt bountifully with thee.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 For thou hast delivered my soul from death, my eyes from tears, my feet from falling.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 I will walk before the Lord in the land of life.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 I believe, therefore will I speak: I was greatly afflicted;
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 I indeed said in my despondency, Every man is a liar.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 What shall I give in return unto the Lord for all his bounties toward me?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 The cup of salvation will I lift up, and on the name of the Lord will I call.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 My vows will I pay unto the Lord, yea, in the presence of all his people.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Grievous in the eyes of the Lord is the death of his pious ones.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 O Lord, truly am I thy servant, I am thy servant, —the son of thy handmaid: thou hast loosened my fetters.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Unto thee will I offer the sacrifice of thanksgiving, and on the name of the Lord will I call.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 My vows will I pay unto the Lord, yea, in the presence of all his people,
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 In the courts of the house of the Lord, in thy midst, O Jerusalem. Hallelujah.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 116 >