< Psalms 108 >
1 “A song or psalm of David.” My heart is firm, O God; I will sing and give praise, even with my spirit.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Awake, psaltery and harp: I will wake up the morning-dawn.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 I will give thee thanks among the people, O Lord: and I will sing praises unto thee among the nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 For great above the heavens is thy kindness, and thy truth reacheth even unto the skies.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Exalt thyself above the heavens, O God; and above all the earth thy glory.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 In order that thy beloved may be delivered: help with thy right hand, and answer me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 God hath spoken in his holiness: I will exult, I will divide Shechem, and the valley of Succoth will I measure out.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Mine id Gil'ad, and mine is Menasseh; Ephraim also is the strong-hold of my head; of Judah are my chiefs.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab is my washpot; upon Edom will I cast my shoe; over Philistia will I triumph.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Who will bring me into the fortified city? who will lead me as far as Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Behold, it is thou, O God, who hast cast us off; and thou, O God, goest not forth with our armies.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Give us help against the assailant; for vain is the help of man.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 Through God shall we do valiantly; for he it is that will tread down our adversaries.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.