< Psalms 103 >

1 “Of David.” Bless, O my soul, the Lord, and all that is within me, his holy name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Bless, O my soul, the Lord, and forget not all his benefits:
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 Who forgiveth all thy iniquities; who healeth all thy diseases;
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 Who redeemeth from the pit thy life; who crowneth thee with kindness and mercies;
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 Who satisfieth with happiness thy spirit, so that thy youth is renewed like the eagle's [plumage].
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 The Lord executeth righteousness, and justice for all that are oppressed.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He made known his ways unto Moses, unto the children of Israel his acts.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 Merciful and gracious is the Lord, long-suffering and abundant in kindness.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 Not for all eternity will he contend; nor will he for ever retain his anger.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 Not in accordance with our sins hath he dealt with us; nor according to our iniquities hath he requited us.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as high as heaven is above the earth, so mighty is his kindness toward those that fear him.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 As far as the east is from the west, so far hath he removed from us our transgressions.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 As a father hath mercy on his children, so hath the Lord mercy on those that fear him.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For he knoweth our frame; he remembereth that we are dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 As for man, like the grass are his days: as the blossom of the field, so doth he bloom.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 When a wind but passeth over it, it is gone, and its place will recognize it no more.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 But the kindness of the Lord is from everlasting to everlasting over those that fear him, and his righteousness unto children's children,
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 To such as keep his covenant, and to those who remember his precepts to execute them.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 The Lord hath established in the heavens his throne; and his kingdom ruleth over all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Bless the Lord, ye his angels, mighty in strength, that execute his word, hearkening unto the voice of his word.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Bless ye the Lord, all his hosts, ye his ministers, that execute his will.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Bless the Lord, all his works, in all the places of his dominion; bless, O my soul, the Lord.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psalms 103 >