< Psalms 102 >

1 “A prayer of the afflicted, when he is overwhelmed, and poureth out before the Lord his complaint.” O Lord, hear my prayer, and let my cry come unto thee.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Hide not thy face from me on the day when I am distressed; incline unto me thy ear; on the day when I call, answer me speedily.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 For my days vanish in smoke, and my bones are burning like a hearth.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Struck [by heat] like the herb and dried up is my heart; for I forget to eat my bread.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Because of the voice of my groaning my bones cleave to my flesh.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 I am like the pelican of the wilderness: I am become like the owl amid ruins.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 I watch, and I am become like a [night-]bird sitting alone upon the housetop.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 All the day my enemies reproach me: they that mock me swear by me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 For ashes do I eat like bread, and my drink I mingle with weeping;
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 Because of thy indignation and thy wrath; for thou hadst lifted me up, and hast cast me down.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 My days are like a shadow that declineth; and like the herb I wither.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 But thou, O Lord, wilt sit enthroned for ever; and thy memorial is unto all generations.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Thou wilt indeed arise; thou wilt have mercy upon Zion; for it is time to favor her, for the appointed time is coming.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 For thy servants hold dear her stones, and her very dust they cherish.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Then shall nations fear the name of the Lord, and all the kings of the earth thy glory:
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 When the Lord shalt have built up Zion, he appeareth in his glory;
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 [When] he hath regarded the prayer of the forsaken, and doth not despise their prayer.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 This shall be written down for the latest generation; and the people which shall be created shall praise the Lord.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 For he hath looked down from the height of his sanctuary; the Lord hath cast from heaven his view to the earth:
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 To hear the sighing of the prisoner; to loosen those that are doomed to death:
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 That men may proclaim in Zion the name of the Lord, and his praise in Jerusalem;
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 When people are gathered together, and kingdoms, to serve the Lord.—
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 He hath weakened on the way my strength; he hath shortened my days.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 I will say, O my God! take me not away in the midst of my days: throughout all generations are thy years.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 In olden times didst thou lay the foundations of the earth; and the heavens are the work of thy hands.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 These will indeed perish, but thou wilt ever exist: yea, all of them will wear out like a garment; as a vesture wilt thou change them, and they will be changed;
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 But thou art ever the same, and thy years will have no end.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 The children of thy servants will dwell [securely], and their seed will be firmly established before thee.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalms 102 >