< Proverbs 31 >
1 The words of king Lemuel, the prophecy with which his mother instructed him.
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 What [hast thou done], O my son: and what, O son of my body? and what, O son of my vows?
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Give not unto women thy vigor, nor thy ways to those that ruin kings.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 Not for kings, O Lemoel, not for kings [it is fitting] to drink wine, nor for princes, strong drink:
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 Lest either might drink, and forget what is written in the law, and pervert the cause of all the afflicted.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Give strong drink unto him that is ready to perish, and wine unto those who have an embittered soul.
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 Let such a one drink, and forget his poverty, and remember his trouble no more.
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Open thy mouth for the dumb, for the cause of all fatherless children.
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Open thy mouth, judge righteously, and decide the cause of the poor and needy.
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 Who can find a virtuous woman: for far above pearls is her value.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 The heart of her husband doth safely trust in her, and he will not see his gain diminish.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 She treateth him well and not ill, all the days of her life.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 She seeketh for wool and flax, and worketh with her willing hands.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 She is become like the merchant's ships: from afar doth she bring her food.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 And she riseth while it is yet night, and giveth provision to her household, and a task to her maidens.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 She thinketh of a field, and buyeth it: with the fruit of her hands she planteth a vineyard.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 She girdeth with strength her loins, and giveth vigor to her arms.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 She perceiveth that her profit is good: [therefore] her lamp goeth not out by night.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 She stretcheth out her hands to the spindle, and her palms hold fast the distaff.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 She spreadeth out wide her open palm to the poor: yea, her hands she stretcheth forth to the needy.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 She hath no fear for her household of the snow: for all her household are clothed in scarlet.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 Tapestry-covering she maketh for herself: of linen and purple is her attire.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Well known is in the gates her husband, when he sitteth with the elders of the land.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 Fine tunics she maketh, and selleth them, and girdles she furnisheth unto the merchant.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 Strength and dignity are her clothing: and she smileth at the coming of the last day.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 She openeth her mouth with wisdom, and the law of kindness is on her tongue.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 She looketh well to the ways of her household, and the bread of idleness she doth not eat.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 Her children rise up, and call her blessed; her husband, also, and he praiseth her:
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 “Many daughters have done virtuously; but thou excellest them all.”
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 False is grace, and vain is beauty: a woman only that feareth the Lord shall indeed be praised.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Give her of the fruit of her hands, and let her own works praise her in the gates.
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.