< Proverbs 20 >
1 Wine is a mocker, strong drink is noisy; and whosoever indulgeth therein will never be wise.
Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
2 Like the roaring of a young lion is the dread of a king: whoso provoketh him to anger sinneth against his own soul.
Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
3 It is an honor for a man to cease from a contest; but every fool enrageth himself.
Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
4 Because it is winter's cold, will the sluggard not plough: when he therefore seeketh in the harvest time, there will be nothing.
Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
5 Like deep water is counsel in the heart of man; but the man of understanding will draw it out.
Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
6 Most men will proclaim every one his own kindness; but who can find a faithful man?
Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
7 The righteous walketh in his integrity: happy will be his children after him.
Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
8 A king that sitteth on the throne of justice scattereth away with his eyes all evil.
Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
9 Who can say, I have made my heart pure, I am cleansed from my sin.
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10 Divers weights, and divers measures, are both of them alike an abomination of the Lord.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11 Even a child maketh himself known by his doings, whether his work will be pure, and whether it will be upright.
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12 The ear that heareth, and the eye that seeth, the Lord hath made both of them alike.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
13 Love not sleep, lest thou come to poverty: open thy eyes, so wilt thou be satisfied with bread.
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
14 It is bad, it is bad, saith the buyer; but when he is gone his way, then doth he boast.
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
15 There is gold, and a multitude of pearls; but a precious vessel are the lips of knowledge.
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
16 Take away his garment, because he hath become surety for a stranger; and on account of a strange woman take a pledge from him.
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
17 Bread of falsehood is pleasant to a man; but afterward his mouth will be filled with gravel-stones.
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
18 Plans are established by counsel; and with wise reflection conduct war.
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
19 He that goeth about as a talebearer revealeth secrets: therefore meddle not with him that enticeth with his lips.
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
20 Whoso curseth his father or his mother—his lamp shall be quenched in obscure darkness.
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21 An inheritance hastily gotten at the beginning will at its end not be blessed,
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22 Do not say, I will recompense evil; [but] wait on the Lord, and he will help thee.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23 Divers weights are an abomination of the Lord; and a deceitful balance is not good.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24 From the Lord are the steps of man [ordained]; but man— how can he understand his own way?
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25 It is a snare to a man to sanctify things hastily, and to make inquiry only after having made vows.
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
26 A wise king scattereth the wicked, and turneth over them the threshing-wheel.
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27 A lamp of the Lord is the soul of man, searching all the inner chambers of the body.
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28 Kindness and truth will watch over a king, and he will prop up through kindness his throne.
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29 The ornament of young men is their strength; and the glory of old men is a hoary head.
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30 The bruises of a wound are cleansing means for the bad, and stripes [will reach] the inner chambers of the body.
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.