< Numbers 3 >

1 And these are the generations of Aaron and Moses, on the day that the Lord spoke with Moses on mount Sinai.
Waɗannan su ne zuriyar Haruna da Musa a lokacin da Ubangiji ya yi magana da Musa a kan Dutsen Sinai.
2 And these are the names of the sons of Aaron: the firstborn Nadab, and Abihu, Elazar, and Ithamar.
Sunayen’ya’yan Haruna su ne, Nadab ɗan fari, da Abihu, da Eleyazar da Itamar.
3 These are the names of the sons of Aaron, the priests that were anointed, who were consecrated to minister as priests.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Haruna, shafaffun firistocin da aka naɗa domin su yi aiki firist.
4 And Nadab and Abihu died before the Lord, when they offered a strange fire before the Lord, in the wilderness of Sinai, and they had no children: and Elazar and Ithamar ministered as priests in the life-time of Aaron their father.
Amma Nadab da Abihu suka fāɗi suka mutu a gaban Ubangiji a Hamadar Sinai a sa’ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta a gabansa. Ba su kuwa da’ya’ya; saboda haka Eleyazar da Itamar kaɗai suka yi aiki firist a zamanin mahaifinsu Haruna.
5 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 Bring the tribe of Levi near, and present the same before Aaron the priest, that they may serve him.
“Ka kawo mutanen Lawi, ka kuma gabatar da su ga Haruna firist, don su taya shi aiki.
7 And they shall keep his charge, and the charge of the whole congregation before the tent of the congregation, to do the service of the tabernacle.
Za su yi wa Haruna da dukan al’umma aikace-aikace a Tentin Sujada, ta wurin yin aikin tabanakul.
8 And they shall keep all the vessels of the tent of the congregation, and the charge of the children of Israel, to do the service of the tabernacle.
Za su lura da dukan kayayyakin Tentin Sujada, suna cika hakkin Isra’ilawa ta wurin yin aiki a tabanakul.
9 And thou shalt give the Levites unto Aaron and to his sons: as associates are they given unto him out of the children of Israel.
Ka ba da Lawiyawa ga Haruna da’ya’yansa; su ne za su zama Isra’ilawan da za a ba da su ɗungum gare shi.
10 And Aaron and his sons shalt thou instruct, that they shall guard well their priest's office; and the stranger that cometh nigh shall be put to death.
Ka naɗa Haruna da’ya’yansa su yi aiki firistoci; duk wanda ya yi shisshigi a wuri mai tsarki kuwa dole a kashe shi.”
11 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
12 And I, behold, I have taken the Levites from the midst of the children of Israel instead of every first-born that openeth the womb among the children of Israel; and the Levites shall be mine.
“Ga shi na ɗauki Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a maimakon ɗan fari na kowace mace a Isra’ila. Lawiyawa nawa ne,
13 Because mine is every first-born; on the day when I smote every first-born in the land of Egypt I hallowed unto me every first-born in Israel, both man and beast: mine shall they be; I am the Lord.
gama duk’ya’yan fari nawa ne. Lokacin da karkashe duk’ya’yan fari a Masar, na keɓe wa kaina kowane ɗan fari a Isra’ila, ko mutum, ko dabba. Za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.”
14 And the Lord spoke unto Moses in the wilderness of Sinai, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai ya ce,
15 Number the children of Levi after their divisions, by their families; every male of them from a month old and upward shalt thou number.
“Ka ƙidaya Lawiyawa bisa ga iyalansu da kabilarsu. Ka ƙidaya kowane ɗan jinjiri mai wata ɗaya ko fiye.”
16 And Moses numbered them according to the order of the Lord, as he had been commanded.
Saboda haka Musa ya ƙidaya su duka, kamar yadda maganar Ubangiji ta umarta.
17 And these were the sons of Levi by their names: Gershon, and Kehath, and Merari.
Ga sunayen’ya’yan Lawi, Gershon, Kohat da Merari.
18 And these are the names of the sons of Gershon after their families: Libni, and Shimi.
Ga sunayen mutanen Gershon, Libni, da Shimeyi
19 And the sons of Kehath after their families: 'Amram, and Yizhar, Chebron, and 'Uzziel.
Sunayen mutanen Kohat kuwa su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.
20 And the sons of Merari after their families: Machli, and Mushi; these are the families of the Levites according to their family divisions.
Dangin Merari su ne. Mali da Mushi. Ga kabilan Lawiyawa bisa ga iyalansu.
21 Of Gershon: the family of the Libnites, and the family of the Shimites; these are the families of the Gershunites.
A wajen Gershonawa, kabilarsa su ne Libniyawa, da Shimeyiyawa; waɗannan su ne mutanen Gershom.
22 Those that were numbered of them, by the numbering of all the males from a month old and upward, even those that were numbered of them, were seven thousand and five hundred.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya zuwa gaba da haihuwa su kai 7,500.
23 The families of the Gershunites used to encamp behind the tabernacle, westward.
Kabilar Gershonawa za su yi sansani ta fuskar yamma, a bayan tabanakul.
24 And the prince of the family division of the Gershunites was Elyassaph the son of Lael.
Eliyasaf ɗan Layel shi ne shugaban iyalan Gershonawa.
25 And the charge of the sons of Gershon in the tabernacle of the congregation was the tabernacle and the tent, its covering, and the hanging for the door of the tabernacle of the congregation,
A Tentin Sujada, Gershonawa su ne za su lura da mazauni da tabanakul da kuma tentin, abubuwan rufensa, labule a ƙofar Tentin Sujada,
26 And the hangings of the court, and the curtain for the door of the court, which is by the tabernacle and by the altar, round about, and its cords for all the service thereof.
da labulen filin da yake kewaye da tabanakul da kuma bagade, da igiyoyi, da kuma kowane abin da ya danganci aikinsu.
27 And of Kehath: the family of the 'Amramites, and the family of the Yizharites, and the family of the Chebronites, and the family of the 'Uzzielites; these are the families of the Kehathites.
Kabilar Kohat su ne, Amramawa da Izharawa da Hebronawa da Uzziyelawa; waɗannan su ne kabilar Kohatawa.
28 By the numbering of all the males, from a month old and upward, they were eight thousand and six hundred, keeping the charge of the sanctuary.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 8,600 ne. Kohatawa ne suke lura da wuri mai tsarki.
29 The families of the sons of Kehath used to encamp on the side of the tabernacle, southward.
Kohatawa za su yi sansani a kudu da tabanakul.
30 And the prince of the division of the families of the Kehathites was Elizaphan the son of 'Uzziel.
Shugaban kabilar Kohatawa shi ne Elizafan ɗan Uzziyel.
31 And their charge was the ark, and the table, and the candlestick, and the altars, and the vessels of the sanctuary which are used for the service, and the vail, and all belonging thereto.
Su ne da hakkin kula da akwatin alkawari, tebur, wurin ajiye fitila, bagade, kayayyakin wuri mai tsarki da ake amfani da su a sujada, labule, da kuma kome da ya danganci aikinsu.
32 And the chief over the princes of the Levites was Elazar the son of Aaron the priest, having the oversight of those that kept the charge of the sanctuary.
Babban shugaban Lawiyawa shi ne Eleyazar ɗan Haruna, firist. An naɗa shi a kan waɗanda suke kula da wuri mai tsarki.
33 Of Merari: the family of the Machlites, and the family of the Mushites; these are the families of Merari.
Kabilar Merari su ne Maliyawa da Mushiyawa; waɗannan su ne kabilar Merari.
34 And those that were numbered of them, by the numbering of all the males, from a month old and upward, were six thousand and two hundred.
Jimillar dukan jarirai maza daga wata ɗaya ko fiye, 6,200 ne.
35 And the chief of the division of the families of Merari was Zuriel the son of Abichayil: they used to encamp on the side of the tabernacle, northward.
Shugaban iyalan Merari shi ne Zuriyel ɗan Abihayil. Za su yi sansani arewa da tabanakul.
36 And under the custody and charge of the sons of Merari were the boards of the tabernacle, and its bars, and its pillars, and its sockets, and all its vessels, and all that belongeth thereto,
Kabilar Merari ne aka sa su lura da katakan tabanakul, sandunanta, dogayen sandunanta, tarukanta, dukan kayan aiki da kowane abin da ya danganci aikinsu,
37 And the pillars of the court round about, and their sockets, and their pins, and their cords.
da ginshiƙai kewaye da filin tare da rammuka da turaku da igiyoyinsu.
38 But those that encamped before the tabernacle toward the east, even before the tabernacle of the congregation toward the rising of the sun, were Moses, and Aaron, and his sons, keeping the charge of the sanctuary for the charge of the children of Israel; and the stranger that came nigh was to be put to death.
Musa da Haruna da’ya’yansu za su yi sansani gabas da tabanakul, wajen fitowar rana; a gaban Tentin Sujada. Su ne da hakkin lura da wuri mai tsarki a madadin Isra’ilawa. Duk wani wanda ba ya wannan aiki, ya kuma kusaci wuri mai tsarki, za a kashe shi.
39 All that were numbered of the Levites, whom Moses numbered with Aaron, at the order of the Lord, according to their families, all the males from a month old and upward, were twenty and two thousand.
Jimillar Lawiyawan da Musa da Haruna suka ƙidaya bisa ga umarnin Ubangiji bisa ga danginsu, haɗe da kowane jariri daga wata ɗaya ko fiye, 22,000 ne.
40 And the Lord said unto Moses, Number all the first-born males of the children of Israel from a month old and upward, and take the number of their names.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ƙidaya dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa maza daga wata ɗaya da kuma fiye ka kuma rubuta sunayensu.
41 And thou shalt take the Levites for me, I am the Lord, instead of all the first-born among the children of Israel; and the cattle of the Levites instead of all the first-born among the cattle of the children of Israel.
Ka ɗauko mini Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ilawa, haka ma na dabbobi na Lawiyawa, a maimakon’ya’yan fari na dabbobin Isra’ilawa. Ni ne Ubangiji.”
42 And Moses numbered, as the Lord had commanded him, all the first-born among the children of Israel.
Haka Musa ya ƙidaya’ya’yan fari na Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
43 And all the first-born males, by the numbering of the names, from a month old and upward, of those that were numbered of them, were twenty and two thousand two hundred and seventy and three.
Jimillar’ya’yan fari maza daga wata ɗaya da kuma fiye, da aka rubuta bisa ga sunayensu, 22,273 ne.
44 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Sai Ubangiji ya kuma yi magana da Musa ya ce,
45 Take the Levites instead of all the first-born among the children of Israel, and the cattle of the Levites instead of their cattle; and the Levites shall be mine: I am the Lord.
“Ka ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari na Isra’ila, dabbobin Lawiyawa kuma a maimakon dabbobinsu. Lawiyawa za su zama nawa. Ni ne Ubangiji.
46 And [for] those that are to be redeemed, the two hundred and seventy and three of the first-born of the children of Israel, who are more than the Levites,
Don a fanshi’ya’yan fari 273 na Isra’ilawa da suka fi Lawiyawa yawa,
47 Thou shalt take five shekels apiece for the poll; after the shekel of the sanctuary shalt thou take, twenty gerahs to the shekel;
ka karɓi shekel biyar domin kowannensu, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, wanda yake da nauyin gera ashirin.
48 And thou shalt give unto Aaron and to his sons the money, [for] those who are to be redeemed of those that are over the number of them.
Ka ba wa Haruna da’ya’yansa kuɗin fansar da ya haura kai na’ya’yan farin Isra’ilawa.”
49 And Moses took the redemption-money of those that were over in number above those who were redeemed by the Levites:
Haka, Musa ya karɓi kuɗin fansar waɗanda suka haura yawan Lawiyawa.
50 Of the first-born of the children of Israel did he take the money; a thousand three hundred and sixty and five shekels, after the shekel of the sanctuary.
Daga’ya’yan fari na Isra’ilawa, ya karɓi azurfa masu nauyin shekel 1,365, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri.
51 And Moses gave the money of those who were redeemed unto Aaron and unto his sons, by the order of the Lord; as the Lord had commanded Moses.
Sa’an nan Musa ya ba da kuɗin fansar ga Haruna da’ya’yansa, yadda maganar Ubangiji ta umarce shi.

< Numbers 3 >