< Numbers 14 >
1 And all the congregation lifted up their voice, and cried aloud; and the people wept that night.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 And all the people murmured against Moses and against Aaron; and the whole congregation said unto them, Oh who would grant that we had died in the land of Egypt! or that we might but die in this wilderness!
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 And wherefore doth the Lord bring us unto yonder land, to fall by the sword? that our wives and our children may become a prey? is it not better for us to return to Egypt?
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 And they said one to another, Let us appoint a chief, and let us return to Egypt.
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Then fell Moses and Aaron on their faces before all the assembly of the congregation of the children of Israel.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 And Joshua, the son of Nun, and Caleb the son of Yephunneh, of those that had spied out the land, rent their garments.
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 And they said unto all the congregation of the children of Israel, as followeth, The land, through which we have passed to spy it out, this land is exceedingly good.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 If the Lord have delight in us, then will he bring us into this land, and give it to us: a land which is flowing with milk and honey.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Only against the Lord do ye not rebel; and then ye need not fear the people of the land; for they are our bread: their shadow is departed from them, while the Lord is with us; fear them not.
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 But all the congregation said to stone them with stones: when the glory of the Lord appeared in the tabernacle of the congregation unto all the children of Israel.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 And the Lord said unto Moses, How long yet shall this people provoke me? and how long yet will they not believe in me, with all the signs which I have shown in the midst of them?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 I will smite them with the pestilence, and root them out, and I will make of thee a nation greater and mightier than they.
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 And Moses said unto the Lord, But when the Egyptian hear, from the midst of whom thou hast brought up in thy might this people; —
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 And when they tell to the inhabitants of this land, who have heard that thou, Lord, art in the midst of this people, that face to face thou, Lord, art seen, and that thy cloud standeth over them, and that in a pillar of cloud thou goest before them by day, and in a pillar of fire by night; —
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 That thou hast killed this people as one man: then will the nations that have heard thy fame, say in this manner,
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 That because the Lord was not able to bring this people into the land which he had sworn unto them, hath he slain them in the wilderness.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 And now, I beseech thee, let the greatness of the power of the Lord be made manifest, as thou hast spoken, saying,
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 The Eternal is long-suffering, and abundant in beneficence, forgiving iniquity and transgression; but who will by no means clear the guilty, visiting the iniquity of the fathers upon the children, upon the third and upon the fourth generation.
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Pardon, I beseech thee, the iniquity of this people, according to the greatness of thy beneficence, and as thou hast been indulgent to this people, from Egypt even until hitherto.
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 And the Lord said, I have pardoned according to thy word.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 But as truly as I live, and as all the earth is filled with the glory of the Lord: —
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 That all the men who have seen my glory, and my signs, which I have displayed in Egypt and in the wilderness, and have tempted me these ten times, and have not hearkened to my voice,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 Shall surely not see the land which I have sworn unto their fathers, yea all those that have provoked me shall not see it.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 But my servant Caleb, as a reward that he had another spirit with him, and followed me fully, —therefore will I bring him into the land whereinto he went; and his seed shall possess it.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 And the Amalekites and the Canaanites dwell in the valley: tomorrow turn you, and set forward into the wilderness by the way to the Red Sea.
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 And the Lord spoke unto Moses and unto Aaron, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 How long [shall indulgence be given] to this evil congregation, that murmur against me? the murmurings of the children of Israel, which they murmur against me, have I heard.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Say unto them, As truly as I live, saith the Lord, as ye have spoken in my ears, so will I do to you:
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 In this wilderness shall your carcasses fall, and all that were numbered of you, according to your whole number, from twenty years old and upward; ye who have murmured against me;
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 Truly ye shall not come into the land, concerning which I have lifted up my hand to let you dwell therein; save Caleb the son of Yephunneh, and Joshua the son of Nun.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 But your little ones of which ye said, They would become a prey, them will I bring in, and they shall know the land which ye have despised.
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 But as for you, your carcasses shall fall in this wilderness.
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 And your children shall wander about in the wilderness forty years, and bear your backslidings, until your carcasses be spent in the wilderness.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 After the number of the days in which ye spied out the land, forty days, yea, each one day for a year, shall ye bear for your iniquities, forty years; and ye shall experience my withdrawal [of protection].
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 I the Lord have spoken it, surely, this will I do unto all this evil congregation that have assembled against me: in this wilderness shall they be spent, and therein shall they die.
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 And the men whom Moses had sent to spy out the land, and who returned, and caused all the congregation to murmur against him, by bringing up an evil report against the land,
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 Even these men, that had brought up the evil report of the land, died by the plague before the Lord.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 But Joshua the son of Nun, and Caleb the son of Yephunneh, remained alive of those men, who had gone to spy out the land.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 And Moses spoke these words unto all the children of Israel; and the people mourned greatly.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 And they rose up early in the morning, and went up to the top of the mountain, saying, Lo, here we are, and we will go up unto the place of which the Lord hath spoken; for we have sinned.
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 And Moses said, Wherefore now do ye transgress the order of the Lord? and it will not prosper.
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Do not go up, for the Lord is not among you; that ye may not be smitten before your enemies.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 For the Amalekites and the Canaanites are there before you, and ye will fall by the sword; since, because ye are turned away from the Lord, the Lord also will not be with you.
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Yet they persisted to go up unto the top of the mountain; but the ark of the covenant of the Lord, and Moses, did not move out of the camp.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Then came down the Amalekites, and the Canaanites that dwelt on that mountain, and smote them, and discomfited them, even unto Chormah.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.