< Nehemiah 11 >

1 And the rulers of the people dwelt at Jerusalem: and the rest of the people cast lots, to bring one of every ten to dwell in Jerusalem the holy city, and the nine parts to [remain] in the [other] cities.
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
2 And the people blessed all the men, that offered themselves voluntarily to dwell at Jerusalem.
Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
3 Now these are the chiefs of the province that dwelt in Jerusalem; but in the cities of Judah dwelt every one in his possession in their cities, [to wit, ] Israel, the priests, and the Levites, and the temple-servants, and the children of Solomon's servants.
Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
4 And at Jerusalem dwelt certain of the children of Judah, and of the children of Benjamin. Of the children of Judah: 'Athayah the son of 'Uzziyah, the son of Zechariah, the son of Amaryah, the son of Shephatyah, the son of Mahalalel, of the children of Perez:
yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
5 And Ma'asseyah the son of Baruch, the son of Kol-chozeh, the son of Chazayah, the son of 'Adayah, the son of Joyarib, the son of Zechariah, the son of Hashiloni;
da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
6 All the sons of Perez that dwelt at Jerusalem were four hundred sixty and eight valiant men.
Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
7 And these are the sons of Benjamin: Sallu the son of Meshullam, the son of Jo'ed, the son of Pedayah, the son of Kolayah, the son of Ma'asseyah, the son of Ithiel, the son of Jessha'yah;
Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
8 And next to him Gabbai, Sallai; nine hundred twenty and eight.
da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
9 And Joel the son of Zichri was overseer over them; and Judah the son of Hassenuah was second over the city.
Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
10 Of the priests: Jedayah the son of Joyarib, Jachin:
Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
11 Serayah the son of Chilkiyah, the son of Meshullam, the son of Zadok, the son of Merayoth, the son of Achitub, the superintendent of the house of God;
da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
12 And their brethren who did the work of the house, eight hundred twenty and two; and 'Adayah the son of Jerocham, the son of Pelalyah, the son of Amzi, the son of Zechariah, the son of Pashchur, the son of Malkiyah;
tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
13 And his brethren, chiefs of the divisions, two hundred forty and two; and 'Amashsai the son of 'Azarel, the son of Achsai, the son of Meshillemoth, the son of Immer;
da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
14 And their brethren, mighty men of valor, one hundred twenty and eight; and the overseer over them was Zabdiel, the son of Haggedolim.
da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
15 Also of the Levites: Shema'yah the son of Chasshub, the son of 'Azrikam, the son of Chashabyah, the son of Bunni;
Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
16 And Shabbethai and Jozabad, of the chiefs of the Levites, had the oversight of the outward business of the house of God;
da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
17 And Matthaniah the son of Micha, the son of Zabdi, the son of Assaph, the principal to begin the thanksgiving at prayer; and Bakbukyah the second among his brethren and 'Abda the son of Shammua', the son of Galal, the son of Jeduthun.
Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
18 All the Levites in the holy city were two hundred eighty and four.
Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
19 And the gatekeepers, Akkub, Talmon and their brethren that watched at the gates, were one hundred seventy and two.
Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
20 And the residue of Israel, of the priests, and the Levites, were in all the cities of Judah, every one in his inheritance.
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21 But the temple-servants dwelt in the hill-fort; and Zicha and Gishpa were over the temple-servants.
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22 And the overseer of the Levites at Jerusalem was 'Uzzi the son of Bani, the son of Chashabyah, the son of Matthanyah, the son of Micha, one of the sons of Assaph, the singers, over the business of the house of God.
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23 For the king's command was obligatory on them; and there was a fixed rate for the singers, the requirement of every day on its day.
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24 And Pethachyah the son of Meshezabel, of the children of Zerach the son of Judah, was at the king's hand in every thing concerning the people.
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
25 And respecting the villages with their fields, some of the children of Judah dwelt at Kiryath-arba' and in its villages, and at Dibon and in its villages, and at Jekabzeel and in its villages.
Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
26 And at Jeshua', and at Moladah, and at Beth-phelet,
Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
27 And at Chazar-shu'al, and at Beer-sheba' and in its villages,
da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
28 And at Ziklag, and at Mechonah and in its villages,
Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
29 And at 'En-rimmon, and at Zor'ah, and at Yarmuth,
Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
30 Zanoach, 'Adullam, and in their villages, at Lachish and its fields, at 'Azekah and in its villages. And they dwelt from Beer-sheba' as far as the valley of Hinnom.
da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
31 And the children of Benjamin [dwelt], beginning from Geba', at Michmash, and 'Ay-ya, and Beth-el, and in their villages,
Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
32 'Anathoth, Nob, 'Ananyah,
da Anatot, da Nob, da Ananiya,
33 Chazor, Ramah, Gittayim.
da Hazor, da Rama, da Gittayim,
34 Chadid, Zebo'im, Neballat,
da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
35 Lod, and Ono, the valley of the carpenters.
da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
36 And of the Levites dwelt certain divisions in Judah, and in Benjamin.
Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.

< Nehemiah 11 >