< Micah 5 >

1 Now gather thyself in troops, O daughter of troops; they lay siege against us: with the rod they smite upon the cheek the judge of Israel.
Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
2 But thou, Beth-lechem Ephratah, the least [though] thou be among the thousands of Judah, [yet] out of thee shall he come forth unto me that is to be ruler in Israel, whose origin is from olden times, from most ancient days.
“Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
3 Therefore will he give them up, until the time that she who travaileth hath brought forth: then shall the remnant of his brethren return with the children of Israel.
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
4 And he shall stand forward and feed [Israel] through the strength of the Lord, through the excellency of the name of the Lord his God: and they shall abide [safely]; for now shall he be great even unto the ends of the earth.
Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
5 And in this [manner] shall there be peace: If Asshur should come into our land; and if he should tread in our palaces, then will we raise up against him seven shepherds, and eight anointed men.
Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
6 And they shall lay waste the land of Asshur with the sword, and the land of Nimrod in the gates of its [cities]: thus will he deliver us from Asshur, if he should come into our land, and if he should tread within our borders.
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
7 And the remnant of Jacob shall be in the midst of many people like dew from the Lord, like showers upon the herbs, that wait not for man, nor hope for the sons of man.
Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
8 And the remnant of Jacob shall be among the nations, in the midst of many people, like a lion among the beasts of the forest, like a young lion among flocks of sheep: who, if he break in, both treadeth down, and teareth in pieces, while none can deliver.
Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
9 High shall thy hand be lifted up above thy adversaries, and all thy enemies shall be cut off.
Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
10 And it shall come to pass on that day, saith the Lord, that I will cut off thy horses out of the midst of thee, and I will destroy thy chariots;
“A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
11 And I will cut off the cities of thy land, and I will throw down all thy strongholds;
Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
12 And I will cut off the arts of witchcraft out of thy hand; and soothsayers shalt thou have no more;
Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
13 And I will cut off thy graven images, and thy statues out of the midst of thee; and thou shalt no more prostrate thyself to the work of thy hands;
Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
14 And I will pluck up thy groves out of the midst of thee; and I will destroy thy enemies.
Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
15 And I will in anger and in fury execute vengeance upon the nations, upon those that have not hearkened.
Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”

< Micah 5 >