< Malachi 4 +
1 For, behold, the day is coming, which shall burn as an oven; and all the presumptuous, yea, and all who practise wickedness shall be stubble: and the day that is coming shall set them on fire, saith the Lord of hosts, who will not leave them root or bough.
“Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 But there shall rise unto you that fear my name the sun of righteousness with healing in his wings: and ye will go forth, and grow fat as calves of the stall.
Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
3 And ye will tread down the wicked; for they shall be ashes under the soles of your feet, on the day that I create, saith the Lord of hosts.
Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Remember ye the law of Moses my servant, whom I commanded on Horeb for all Israel, statutes and ordinances.
“Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
5 Behold, I send unto you Elijah the prophet before the coming of the day of the Lord, the great and the dreadful.
“Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
6 And he shall turn back the heart of the fathers to the children, and the heart of the children to their fathers: lest I come and smite the earth with a curse.
Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”