< Malachi 1 >

1 The prophecy of the word of the Lord to Israel by means of Malachi.
Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
2 I have loved you, so hath said the Lord: yet ye say, Wherein hast thou loved us? Is not Esau brother to Jacob? saith the Lord: yet I loved Jacob;
“Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
3 And Esau I hated; and I rendered his mountains a desert, and his heritage a dwelling for the monsters of the wilderness.
amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
4 Should Edom even say, We are impoverished; but we will return and build the ruined places: thus hath said the Lord of hosts, They may indeed build, but I will surely throw down; and men shall call them, The territory of wickedness, and, The people against whom the Lord hath indignation to eternity.
Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
5 And your eyes shall see it; and ye shall then say, The Lord will be magnified beyond the territory of Israel.
Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
6 A son honoreth his father, and a servant his master: if then I be a father, where is my honor? and if I be a master, where is my fear? saith the Lord of hosts unto you, O priests, that despise my name; and ye say, wherein have we despised thy name?
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
7 Ye offer upon my altar polluted bread; and ye say, Wherein have we polluted thee? In that ye say, The table of the Lord is contemptible.
“Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
8 And if ye bring near the blind to sacrifice it, is this not evil? and if ye bring near the lame and the sick, is this not evil? do but present it unto thy governor, will he be pleased with thee, or receive thee with favor? saith the Lord of hosts.
Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 And now, I pray you, beseech the presence of God that he may be gracious unto us; from your hand hath this thing come: will he receive one of you with favor? saith the Lord of hosts.
“To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
10 Oh that there were some one among you that would lock up the doors [of the sanctuary], that ye might not light up my altar for nought: I have no pleasure in you, saith the Lord of hosts, neither will I accept in favor an offering from your hand.
“Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 For from the rising of the sun even unto his going down my name is great among the nations; and in every place incense is burnt and there is offered unto my name, even a pure offering; for great is my name among the nations, saith the Lord of hosts.
Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 But ye profane it, in that ye say, The table of the Lord is polluted, and by the assertion, Its food is contemptible.
“Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
13 And ye have said, Behold, what a wearisome task is it! and ye have left it to famish, saith the Lord of hosts; and ye have brought what was robbed, and the lame, and the sick, and thus ye have brought an offering: should I accept this in favor from your hand? saith the Lord.
Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
14 But cursed be the deceiver, who hath in his flock a male, and voweth, and sacrificeth a corrupt thing unto the Lord; for I am a great king, saith the Lord of hosts, and my name is feared among the nations.
“La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.

< Malachi 1 >