< Leviticus 8 >

1 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Take Aaron and his sons with him, and the garments, and the anointing oil, and the bullock for the sin-offering, and the two rams, and the basket of unleavened bread;
“Kawo Haruna da’ya’yansa maza, ka ɗauki rigunansu, man keɓewa, bijimi domin hadaya don zunubi,’yan raguna biyu da kuma kwandon da yake da burodi marar yisti,
3 And all the congregation shalt thou assemble together unto the door of the tabernacle of the congregation.
ka kuma tara dukan jama’a a ƙofar Tentin Sujada.”
4 And Moses did as the Lord had commanded him; and the assembly came together unto the door of the tabernacle of the congregation.
Sai Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi, jama’a kuwa suka taru a ƙofar Tentin Sujada.
5 And Moses said unto the congregation, This is the thing which the Lord hath commanded to do.
Sai Musa ya ce wa jama’ar, “Ga abin da Ubangiji ya umarta a yi.”
6 And Moses brought near Aaron and his sons, and washed them with water.
Sa’an nan Musa ya kawo Haruna da’ya’yansa maza gaba, ya kuma wanke su da ruwa.
7 And he put upon him the coat, and girded him with the girdle, and clothed him with the robe, and put upon him the ephod, and he girded him with the belt of the ephod, and bound it unto him therewith.
Ya sa wa Haruna taguwa, ya ɗaura igiya kewaye da shi, ya sa masa riga, ya sa masa efod. Ya kuma ɗaura masa efod wanda aka yi masa saƙar gwaninta.
8 And he put on him the breastplate; and he put in the breastplate the Urim and the Thummim.
Ya sa masa ƙyallen maƙalawa a ƙirji, ya kuma sa Urim da Tummim a ƙyallen maƙalawa a ƙirjin.
9 And he put the mitre upon his head; and he placed upon the mitre, toward the front thereof, the golden plate, the holy crown; as the Lord had commanded Moses.
Sai ya naɗa masa rawani, daga gaban rawanin ya sa allon zinariya, wato, kambi tsattsarka, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
10 And Moses took the anointing oil, and anointed the tabernacle and all that was therein, and sanctified them.
Sa’an nan Musa ya ɗauki man keɓewa ya keɓe tabanakul da kuma kowane abin da yake cikinsa, ta haka ya tsarkake su.
11 And he sprinkled thereof upon the altar seven times; and he anointed the altar and all its vessels, also the laver and its foot, to sanctify them.
Ya yayyafa mai a kan bagade sau bakwai, yana keɓe bagade da dukan kayayyaki, da daro, da abin da yake tsaya a kai, don yă tsarkake su.
12 And he poured of the anointing oil upon Aaron's head, and he anointed him, to sanctify him.
Ya zuba man keɓewa a kan Haruna, ya kuma keɓe shi don yă tsarkake shi.
13 And Moses brought near the sons of Aaron, and clothed them with coats, and girded them with girdles, and bound the bonnets on them; as the Lord had commanded Moses.
Sa’an nan ya kawo’ya’yan Haruna maza, ya sa musu taguwoyi, ya ɗaɗɗaura igiyoyi kewaye da su, ya kuma sa musu huluna yadda Ubangiji ya umarce shi.
14 And he brought near the bullock of the sin-offering: and Aaron and his sons laid their hands upon the head of the bullock of the sin-offering.
Sa’an nan ya miƙa bijimi domin hadaya don zunubi, sai Haruna da’ya’yansa suka ɗibiya hannuwansu a bijimin.
15 And some one slew him; and Moses took the blood, and put it upon the horns of the altar round about with his finger, and purified the altar, and the [remaining] blood he poured out at the bottom of the altar, and sanctified it, to make henceforth atonement upon it.
Musa ya yanka bijimin ya ɗauki jinin, ya sa yatsarsa ya zuba a dukan ƙahonin bagade don yă tsarkake bagaden. Ya zuba sauran jinin a gindin bagade. Ta haka ya tsarkake shi don yă yi kafara dominsa.
16 And he took all the fat that was upon the inwards, and the midriff of the liver, and the two kidneys, and their fat, and Moses burnt them upon the altar.
Musa ya ɗebo dukan kitsen da yake kewaye da kayan ciki, da kuma wanda ya rufe hanta, da ƙodojin, da kuma kitsensu, ya kuma ƙone su a kan bagade.
17 But the bullock, and his hide, and his flesh, and his dung, he burnt with fire without the camp; as the Lord had commanded Moses.
Amma bijimin da fatarsa da namansa da kuma ƙashinsa ya ƙone su a bayan sansani, yadda Ubangiji ya umarce shi.
18 And he brought near the ram of the burnt-offering; and Aaron and his sons laid their hands upon the head of the ram.
Sa’an nan ya miƙa ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan rago.
19 And some one killed him; and Moses sprinkled the blood upon the altar round about.
Sa’an nan Musa ya yanka ɗan ragon, ya kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagaden.
20 And the ram he cut into the proper pieces; and Moses burnt the head, and the pieces, and the fat.
Ya yanka ragon gunduwa-gunduwa ya ƙone kan, ya kuma ƙone gunduwa-gunduwan da kitsen.
21 And he washed the inwards and the legs in water; and Moses burnt the whole ram upon the altar: it was a burnt-sacrifice for a sweet savor, an offering made by fire unto the Lord; as the Lord had commanded Moses.
Ya wanke kayan cikin da ƙafafun a ruwa, ya kuma ƙone dukan ragon a bisa bagade kamar hadaya ta ƙonawa, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 And he brought near the other ram, the ram of consecration; and Aaron and his sons laid their hands upon the head of the ram.
Sai ya miƙa ɗayan ɗan ragon, ɗan ragon naɗin, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan ragon.
23 And some one slew him; and Moses took some of his blood, and put it upon the tip of Aaron's right ear, and upon the thumb of his right hand, and upon the great toe of his right foot.
Musa kuwa ya yanka ɗan ragon ya ɗibi jinin ya sa leɓatun kunnen dama na Haruna, ya kuma sa a babbar yatsarsa ta hannun dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama.
24 And he brought near Aaron's sons, and Moses put some of the blood upon the tip of their right ear, and upon the thumb of their right hand, and upon the great toe of their right foot; and Moses sprinkled the blood upon the altar round about.
Musa ya kuma kawo’ya’yan Haruna gaba, ya sa jini a leɓatun kunnuwansu na dama, ya kuma sa a manyan yatsotsinsu na hannun dama da kuma a manyan yatsotsinsu na ƙafafunsu na dama. Sa’an nan ya yayyafa jinin a kowane gefen bagade.
25 And he took the fat, and the rump, and all the fat that was upon the inwards, and the midriff of the liver, and the two kidneys, and their fat, and the right shoulder;
Ya ɗibi kitsen, da wutsiya mai kitse, da kuma dukan kitsen da ke kewaye da kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, ƙodoji biyu da kitsensu da kuma cinya ta dama.
26 And out of the basket of unleavened bread, that was before the Lord, he took one unleavened cake, and one cake of oiled bread, and one wafer, and he put them on the fat, and upon the right shoulder;
Sa’an nan daga cikin kwandon burodi marar yisti wanda yake a gaban Ubangiji, ya ɗauko dunƙulen burodi, da kuma guda da aka yi da mai, da kuma ƙosai; ya sa waɗannan a sassan kitsen, da kuma a cinya ta dama.
27 And he placed the whole upon the hands of Aaron, and upon the hands of his sons, and made with them a waving before the Lord.
Ya sa waɗannan a hannuwan Haruna da’ya’yansa, suka kuma kaɗa su a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
28 And Moses then took these things from off their hands, and burnt them on the altar upon the burnt-offering: they were a consecration-offering for a sweet savor, a fire-offering were they unto the Lord.
Sa’an nan Musa ya karɓe su daga hannuwansu ya ƙone a bagade a bisa hadaya ta ƙonawa a matsayin hadaya ta naɗi, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
29 And Moses took the breast, and made therewith a waving before the Lord; from the ram of consecration was it given to Moses as his portion; as the Lord had commanded Moses.
Ya kuma ɗauki ƙirjin; rabon Musa na ɗan ragon naɗi, ya kaɗa shi a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 And Moses took some of the anointing oil, and of the blood which was upon the altar, and sprinkled the same upon Aaron, and upon his garments, and upon his sons, and his sons with sanctified upon the garments of him; and he Aaron, his garments, and his sons, and the garments of his sons with him.
Sai Musa ya ɗibi man keɓewa da jini daga bagade, ya yayyafa su a kan Haruna da rigunansa, da kuma a kan’ya’yansa da rigunansu, don yă tsarkake Haruna da rigunansa da kuma’ya’yansa da rigunansu.
31 And Moses said unto Aaron and to his sons, Boil ye the flesh at the door of the tabernacle of the congregation; and there shall ye eat it with the bread that is in the basket of the consecration; as I have commanded, saying, Aaron and his sons shall eat it.
Sai Musa ya ce wa Haruna da’ya’yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar Tentin Sujada, ku kuma ci shi a can tare da burodi daga kwandon naɗi, yadda na umarta, cewa, ‘Haruna da’ya’yansa maza za su ci shi.’
32 And that which is left of the flesh and of the bread shall ye burn with fire.
Sa’an nan ku ƙone sauran naman da kuma burodin.
33 And from the door of the tabernacle of the congregation shall ye not go forth seven days, until the days of your consecration be at an end; for seven days shall your consecration last.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada har kwana bakwai, sai ranakun naɗi suka cika, gama naɗinku zai ɗauki kwana bakwai.
34 As they have done this day, so hath the Lord commanded to do farther, to make an atonement for you.
Abin da aka yi a yau umarni ne daga Ubangiji don yin kafara saboda ku.
35 And at the door of the tabernacle of the congregation shall ye abide day and night seven days, and keep the charge of the Lord, that ye die not; for so have I been commanded.
Dole ku kasance a ƙofar Tentin Sujada dare da rana har kwana bakwai, ku kuma yi abin da Ubangiji yake bukata, don kada ku mutu; gama abin da aka umarce ni ke nan.”
36 And Aaron and his sons did all the things which the Lord had commanded by the hand of Moses.
Saboda haka Haruna da’ya’yansa maza suka yi kome da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Leviticus 8 >