< Leviticus 26 >

1 Ye shall not make yourselves any idols, and a graven image, or a standing image shall ye not rear up unto you, and any carved stone shall you not place in your land, to bow down upon it; for I am the Eternal your God.
“‘Kada ku yi gumaka, ko ku kafa siffa, ko al’amudi wa kanku, kada kuma ku sa sassaƙaƙƙun duwatsu a ƙasarku don ku rusuna musu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
2 My sabbaths shall ye keep, and my sanctuary shall ye reverence: I am the Lord.
“‘Ku kiyaye Asabbataina, ku kuma ba wa wuri mai tsarkina girma. Ni ne Ubangiji.
3 If in my statutes ye walk, and if my commandments ye keep, and do them:
“‘In kuka kiyaye farillaina, kuka yi biyayya da umarnaina,
4 Then will I give you rains in their due season, and the earth shall yield her products, and the tree of the field shall yield its fruit.
zan aika da ruwan sama a lokacinsa, ƙasa kuma za tă ba da hatsi, itatuwa kuma za su haihu’ya’yansu.
5 And the threshing shall reach with you unto the vintage, and the vintage shall reach unto sowing-time; and ye shall eat your bread to the full, and ye shall dwell in safety in your land.
Masussukanku za su ci gaba har lokacin girbin inabi, girbin inabi kuma zai ci gaba har lokacin shuki, za ku kuma ci duk abincin da kuke so cikin salama a ƙasarku.
6 And I will give peace in the land, and ye shall lie down, with none to make you afraid; and I will remove evil beasts out of the land, and the sword shall not pass through your land.
“‘Zan ba ku salama a ƙasar, za ku kuwa kwanta, kuma babu wani da zai tsorata ku. Zan kori mugayen namun jeji daga ƙasar, takobi kuma ba zai ratsa cikin ƙasarku ba.
7 And ye shall chase your enemies, and they shall fall before you by the sword.
Za ku kori abokan gābanku, za su kuwa fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
8 And five of you shall chase a hundred, and a hundred of you shall chase ten thousand; and your enemies shall fall before you by the sword.
Mutanenku biyar za su kori mutum ɗari, mutanenku ɗari kuma za su kori mutane dubu goma, abokan gābanku kuma za su fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
9 And I will turn myself unto you, and make you fruitful, and multiply you; and I will establish my covenant with you.
“‘Zan dube ku da idon rahama, in kuma sa ku riɓaɓɓanya ku kuma ƙaru, zan kiyaye alkawarina da ku.
10 And ye shall eat very old store, and the old shall ye remove away because of the new.
Za ku ci gaba da cin girbin bara, har ku fitar da shi don ku sami wurin saboda sabo.
11 And I will set my dwelling among you; and my soul shall not loath you.
Zan kafa wurin zamana a cikinku, ba zan kuma yi ƙyamarku ba.
12 And I will walk among you, and I will be to you a God, and ye shall be to me a people.
Zan yi tafiya a cikinki in kuma zama Allahnku, za ku kuwa zama mutanena.
13 I am the Eternal your God, who have brought you forth out of the land of Egypt, that ye should not be their bond-men; and I have broken the bands of your yoke, and caused you to walk upright.
Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar don kada ku ƙara zama bayi ga Masarawa; na karya sandunan wahalarku, na kuma bar ku ku yi tafiya a sake.
14 But if ye will not hearken unto me, and will not do all these commandments;
“‘Amma in za ku kasa kunne gare ni, ku kuma aikata dukan waɗannan umarnai,
15 And if my statutes ye despise, and if my ordinances your soul loath, so as not to do all my commandments, in that ye break my covenant:
in kuka kuma ƙi farillaina, kuka yi ƙyamar dokokina, kuka kuma kāsa kiyaye umarnaina, har kuka karya alkawarina,
16 Then will I also do this unto you, and I will inflict on you terror, consumption, and the burning ague, that consume the eyes, and cause sorrow of heart; and ye shall sow in vain your seed, for your enemies shall eat it.
to, zan yi muku wannan. Zan kawo muku abin bantsoro, cututtuka da zazzaɓin da zai lalatar da idonku, yă kuma sa ranku a wahala. Za ku shuka iri a banza, domin abokan gābanku ne za su ci.
17 And I will set my face against you, and ye shall be struck down before your enemies: and they that hate you shall bear rule over you; and ye shall flee while there is no one pursuing you.
Zan yi gāba da ku har abokan gābanku su ci ku a yaƙi, su waɗanda suke ƙinku za su yi mulki a kanku, za ku gudu ba tare da wani yana korinku ba.
18 And if with these things even ye will not yet hearken unto me: then will I chastise you yet more, sevenfold for your sins.
“‘In bayan dukan wannan, ba ku saurare ni ba, zan hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
19 And I will break the pride of your power; and I will make your heaven as iron, and your earth as copper:
Zan karya ikonku wanda kuke fariya da shi, in hana ruwan sama, ƙasa kuma tă zama kamar tagulla.
20 And in vain shall your strength be spent; for your land shall not yield her products, and the tree of the land shall not yield its fruit.
Ƙarfinku zai ƙare a banza domin ƙasarku ba za tă ba da hatsi ba, balle itatuwan ƙasar su ba da’ya’ya.
21 And if ye walk yet contrary unto me, and if you refuse to hearken unto me: then will I bring more plagues upon you, sevenfold according to your sins.
“‘In kuka ci gaba da tayar mini, kuka ƙi ku saurare ni, zan ninka wahalolinku sau bakwai, yadda ya dace da zunubanku.
22 And I will send out against you the beasts of the field, which shall rob you of your children, and destroy your cattle, and diminish yourselves; so that your roads shall be desolate.
Zan aika da mugayen namun jeji a kanku, za su kuwa kashe’ya’yanku, su hallaka shanunku, su rage yawanku, ku zama kaɗan. Wannan zai sa a rasa mutane a kan hanyoyinku.
23 And if notwithstanding these things ye will not be reformed by me, and walk contrary unto me:
“‘In duk da waɗannan abubuwa, ba ku yarda da gyaran da nake yi muku ba, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
24 Then will I also walk contrary unto you, and I also will punish you, sevenfold for your sins.
zan yi adawa da ku, zan kuma aukar muku saboda zunubanku har sau bakwai.
25 And I will bring over you the sword, avenging the quarrel of my covenant, so that ye shall be gathered together within your cities; and then will I send the pestilence among you, that ye shall deliver yourselves into the hand of the enemy;
Zan kawo takobi a kanku don in yi ramuwa saboda karya alkawarin da kuka yi. Sa’ad da kuka janye zuwa cikin biranenku, zan aika da annoba a cikinku, za a kuwa ba da ku ga hannun abokan gāba.
26 When I break unto you the staff of bread; and ten women shall bake your bread in one oven, and they shall deliver your bread again by weight; and ye shall eat, and not be satisfied.
Sa’ad da na yanke abincinku, mata goma za su dafa abinci a murhu ɗaya, za su kuma rarraba abincin a ma’auni. Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba.
27 And if notwithstanding this ye will not hearken unto me, but walk contrary unto me:
“‘In duk da haka kuka ci gaba da ƙin saurare ni, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
28 Then will I also walk contrary unto you in fury; and I, even I, will chastise you, sevenfold for your sins.
cikin fushina, sai in yi adawa da ku, in kuma hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
29 And ye shall eat the flesh of your sons, and the flesh of your daughters shall ye eat.
Za ku ci naman’ya’yanku maza da na’ya’yanku mata.
30 And I will destroy your high-places, and cut down your sun-images, and cast your carcasses upon the carcasses of your idols; and my soul shall loath you.
Zan rurrushe dukan masujadanku, in yanke bagadanku na turare, in yi tarin gawawwakinku a kan gumakanku, zan kuma yi ƙyamarku.
31 And I will render your cities a waste, and I will make desolate your sanctuaries, and I will not smell the savor of your sweet odors.
Zan mai da biranenku kango, in lalace wuraren tsarkinku, ba zan kuma shaƙi ƙanshi hadayunku ba.
32 And I will surely make desolate the land: and your enemies who dwell therein shall be astonished at it.
Zan mai da ƙasarku kango har abokan gābanku da suke zama a wurin su yi mamaki.
33 And you will I scatter among the nations, and I will draw out after you the sword; and your land shall be a desolate wild, and your cities shall be a waste.
Zan watsar da ku cikin al’ummai, in kuma ja takobina in kore ku. Ƙasarku za tă zama kufai, biranenku kuma su zama kango.
34 Then shall the land satisfy its sabbaths, all the days of its desolation, when ye are in the land of your enemies: then shall the land rest, and satisfy its sabbaths.
Sa’an nan ƙasar za tă ji daɗin hutun shekarun Asabbacinta, a dukan lokutan da take kango, ku kuwa kuna a ƙasar abokan gābanku, sa’an nan ƙasar za tă huta ta ji daɗin asabbatanta.
35 All the days of its desolation shall it rest, the time which it did not rest in your sabbaths, when ye dwelt upon it.
A dukan lokutan da take kango, ƙasar za tă sami hutun da ba tă samu a lokutan asabbatan da kuke zama a cikinta ba.
36 And regarding those that are left of you, I will send a faintness into their hearts in the lands of their enemies; and the sound of a leaf shaken shall chase them; and they shall flee, as fleeing from the sword; and they shall fall with none pursuing.
“‘Ga waɗanda za su ragu kuwa, zan cika zukatansu da tsoro a ƙasashen abokan gābansu har motsin ganyen da iska ta hura zai sa su ruga da gudu. Za su yi gudu kamar suna gudu daga takobi ne, za su kuma fāɗi, ko da yake babu wanda yake korinsu.
37 And they shall stumble one over the other, as before the sword, without one pursuing: and ye shall have no power to stand up before your enemies.
Za su yi karo da juna kamar waɗanda suke tsere wa takobi, ko da yake babu wanda yake korinsu. Ta haka ba za ku iya tsaya a gaban abokan gābanku ba.
38 And ye shall be lost among the nations, and the land of your enemies shall consume you.
Za ku mutu a cikin al’ummai, ƙasar abokan gābanku za tă cinye ku.
39 And they that are left of you shall pine away in their iniquity in the land of your enemies; and also through the iniquities of their fathers shall they pine away with them.
Sauranku da suka ragu za su lalace a ƙasashen abokan gābansu saboda zunubansu; da kuma saboda zunuban kakanninsu.
40 And they shall then confess their iniquity, and the iniquity of their fathers, [that] through their trespass which they trespassed against me, and also that [because] they had walked contrary unto me:
“‘Amma in suka tuba daga zunubansu da zunuban kakanninsu, da cin amanar da suka yi mini, da kuma adawar da suka yi da ni,
41 I also had to walk contrary unto them, and to bring them into the land of their enemies; and then shall their uncircumcised heart be humbled, and then shall they satisfy their iniquity.
waɗanda suka sa na yi adawa da su har da na aika da su ƙasar abokan gābansu, sa’ad da suka ƙasƙantar da zukatansu marasa kaciya, suka kuma biya hukuncin zunubansu,
42 And I will then remember my covenant with Jacob, and also my covenant with Isaac, and also my covenant with Abraham will I remember; and the land will I remember.
zan tuna da alkawarina da Yaƙub, da alkawarina da Ishaku, da kuma alkawarina da Ibrahim, zan tuna da ƙasar.
43 For the land shall be forsaken by them, and shall satisfy its sabbaths, while it lieth desolate without them, and they shall satisfy their iniquity; because, even because my ordinances they despised, and my statutes their soul loathed.
Gama za su gudu su bar ƙasar, ƙasar kuwa ta ji daɗin asabbatanta yayinda take kango muddin ba su ciki. Za su biya hukuncin zunubansu domin sun ƙi dokokina, suka kuma yi ƙyamar farillaina.
44 And yet for all that, though they be in the land of their enemies, will I not cast them away, neither will I loath them, to destroy them utterly, to break my covenant with them; for I am the Lord their God.
Duk da haka, sa’ad da suke a ƙasar abokan gābansu, ba zan ƙi su, ko in yi ƙyamarsu, in hallaka su ƙaƙaf, har in karya alkawarina da su ba. Ni ne Ubangiji Allahnsu.
45 But I will remember for their sakes the covenant of their ancestors, whom I brought forth out of the land of Egypt before the eyes of the nations, that I might be unto them a God: I am the Lord.
Amma saboda su, zan tuna da alkawarin da na yi da kakanninsu, waɗanda na fitar da su daga Masar a idon al’ummai, don in zama Allahnsu. Ni ne Ubangiji.’”
46 These are the statutes and ordinances and laws, which the Lord made between him and the children of Israel on mount Sinai, by the hand of Moses.
Waɗannan su ne farillai, da dokoki, da kuma ƙa’idodin da Ubangiji ya kafa a Dutsen Sinai, tsakaninsa da Isra’ilawa ta wurin Musa.

< Leviticus 26 >