< Judges 21 >
1 Now the men of Israel had sworn in Mizpah, saying, Not any of us shall give his daughter unto Benjamin for wife.
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 And the people came to Beth-el, and abode there till the evening, before God, and they lifted up their voices, and wept with a great lamentation;
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 And they said, Wherefore, O Lord, God of Israel, is this come to pass in Israel, that there should be lacking this day out of Israel one tribe?
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 And it came to pass on the morrow, that the people rose early, and built there an altar, and offered burnt-offerings and peace-offerings.
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 And the children of Israel said, Who is there among all the tribes of Israel that came not up with the congregation unto the Lord? For there had been taken the great oath concerning him that came not up to the Lord to Mizpah, saying, He shall surely be put to death.
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 And the children of Israel felt regret for Benjamin their brother, and they said, One tribe hath this day been cut down from Israel.
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 What shall we do as respecteth wives for those that remain, since we have sworn by the Lord that we will give none of our daughters unto them for wives?
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 And they said, what one is there of the tribes of Israel that came not up unto the Lord to Mizpah? And, behold, there had not come to the camp a man from Yabesh-gil'ad to the assembly.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 For the people were numbered, and, behold, there was not present a man of the inhabitants of Yabesh-gil'ad.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 And the congregation sent thither twelve thousand persons of the valiant men, and commanded them, saying, Go and smite the inhabitants of Yabesh-gil'ad with the edge of the sword, with the women and the children.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 And this is the thing that ye shall do, every male, and every woman that hath known [man] by lying with him, shall ye devote.
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 And they found among the inhabitants of Yabesh-gil'ad four hundred young virgins that had not known man by lying with any male: and they brought them unto the camp to Shiloh, which is in the land of Canaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 And the whole congregation sent and spoke to the children of Benjamin that were on the rock Rimmon, and offered them peace.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 And Benjamin returned at that time: and they gave unto them the wives whom they had saved alive out of the women of Yabesh-gil'ad; but they found not sufficient for them in this way.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 And the people felt regret for Benjamin; because that the Lord had made a breach in the tribes of Israel.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 And the elders of the congregation said, What shall we do for those that remain as respecteth wives; because the women have been destroyed out of Benjamin?
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 And they said, Their inheritance must be secured for Benjamin, that not a tribe may be blotted out from Israel.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 Nevertheless we ourselves are not able to give them wives of our daughters; for the children of Israel have sworn, saying, Cursed be he that giveth a wife to Benjamin.
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 And they said, Behold, there is a feast of the Lord in Shiloh from year to year [at a place] which is on the north side of Beth-el, on the east side of the highway that goeth up from Beth-el to Shechem, and on the south of Lebonah.
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 And they commanded the children of Benjamin, saying, Go ye and lie in wait in the vineyards;
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 And look out, and, behold, if the daughters of Shiloh go out to dance in dances: then come ye forth out of the vineyards, and snatch you every man his wife from the daughters of Shiloh, and go then to the land of Benjamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 And it shall be, when their fathers or their brothers come to contend with us, that we will say unto them, Be favorable unto them for our sakes; because we took not for each man his wife in the war; [and] because ye yourselves did not give them unto them, that ye should at this time be guilty.
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 And the children of Benjamin did so, and took themselves wives, according to their number, from the dancers whom they had stolen away; and they went and returned unto their inheritance, and rebuilt the cities, and dwelt in them.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 And the children of Israel departed thence at that time, every man to his tribe and to his family, and they went out from there every man to his inheritance.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 In those days there was no king in Israel: every man did what was right in his own eyes.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.