< Judges 2 >

1 And a messenger of the Lord came up from Gilgal to Bochim, And he said, I caused you to go up out of Egypt, and I brought you unto the land which I had sworn unto your fathers; and I said, I will not break my covenant with you for ever.
Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
2 But ye for your part shall make no covenant with the inhabitants of this land; their altars shall ye throw down; but ye have not obeyed my voice: what is this ye have done?
ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
3 And I also have said, I will not drive them out from before you; but they shall be evil neighbors to you, and their gods shall become a snare unto you.
Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
4 And it came to pass, when the messenger of the Lord spoke these words unto all the children of Israel, that the people lifted up their voice, and wept.
Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
5 And they called the name of that place, Bochim; and they sacrificed there unto the Lord.
sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
6 And when Joshua had let the people go, the children of Israel went every man unto his inheritance to take possession of the land.
Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
7 And the people served the Lord all the days of Joshua, and all the days of the elders that lived many days after Joshua, who had seen all the great deeds of the Lord, which he had done for Israel.
Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
8 Then died Joshua the son of Nun, the servant of the Lord, being one hundred and ten years old.
Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
9 And they buried him on the border of his inheritance in Timnath-cheres, in the mountain of Ephraim, on the north side of mount Ga'ash.
Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
10 And also all that generation were gathered unto their fathers; and there arose another generation after them, who knew not the Lord, and likewise not the deeds which he had done for Israel.
Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
11 And the children of Israel did the evil in the eyes of the Lord, and served the Be'alim:
Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
12 And they forsook the Lord the God of their fathers, who had brought them out of the land of Egypt, and they went after other gods, of the gods of the nations that were round about them, and they bowed themselves unto them, and incensed the Lord.
Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
13 And they forsook the Lord, and served Baal and 'Ashtaroth.
domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
14 And the anger of the Lord was kindled against Israel, and he delivered them into the hand of spoilers who spoiled them, and he sold them into the hand of their enemies round about, and they were not able any longer to stand before their enemies.
Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
15 Whithersoever they went out, the hand of the Lord was against them for evil, as the Lord had spoken, and as the Lord had sworn unto them: and they were greatly distressed.
Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
16 And the Lord raised up judges, and they delivered them out of the hand of those that spoiled them.
Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
17 But also unto their judges they did not hearken; but they went astray after other gods, and bowed themselves unto them: they turned quickly out of the way which their fathers had walked in, to obey the commandments of the Lord; they did not so.
Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
18 And when the Lord raised them up judges, then was the Lord with the judge, and he delivered them out of the hand of their enemies all the days of the judge; for the Lord bethought himself because of their groaning by reason of those that oppressed them and ill-treated them.
Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
19 And it came to pass, when the judge died, that they returned, and became more corrupt than their fathers, in going after other gods to serve them, and to bow down unto them: they omitted nothing from their doings, and from their stubborn way.
Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
20 And the anger of the Lord was kindled against Israel; and he said, For the cause that this people have transgressed my covenant which I commanded their fathers, and have not hearkened unto my voice:
Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
21 So will I also for my part not drive out henceforth any man from before them out of the nations which Joshua left when he died;
ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
22 In order to prove through them the Israelites, whether they will keep the way of the Lord, to walk therein, as their fathers did keep it, or not.
Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
23 And thus did the Lord leave these nations, so as not to drive them out speedily; and he delivered them not into the hand of Joshua.
Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.

< Judges 2 >