< Judges 15 >
1 And it came to pass after some time, in the time of wheat-harvest, that Samson visited his wife with a kid; and he said, Let me go in to my wife into the chamber; but her father would not suffer him to go in.
Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
2 And her father said, I verily thought that thou didst utterly hate her; therefore I gave her to thy companion: is not her younger sister fairer than she? Let her be thine, I pray thee, instead of her.
Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
3 And Samson said to them, Now shall I be more blameless than the Philistines, though I do them evil.
Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
4 And Samson went and caught three hundred foxes, and took torches, and turned tail to tail, and put one torch between two tails in the midst;
Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
5 And he set the torches on fire, and let them go into the standing corn of the Philistines, and burnt up both shocks and standing corn, as also olive-yards.
sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
6 Then said the Philistines, Who hath done this! And they answered, Samson, the son-in-law of the Thimnite, because he hath taken his wife, and given her to his companion. And the Philistines went up, and burnt her and her father with fire.
Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
7 And Samson said unto them, Since ye will do the like of this, I will surely be avenged on you, and after that will I cease.
Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
8 And he smote them hip and thigh with a great slaughter; and he went down and tarried in the cleft of the rock 'Etam.
Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
9 And the Philistines went up, and encamped in Judah, and spread themselves in Lechi.
Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
10 And the men of Judah said, Why are ye come up against us? And they answered, To bind Samson are we come up, to do to him as he hath done to us.
Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
11 Thereupon went three thousand men of Judah down to the cleft of the rock 'Etam, and said to Samson, Knowest thou not that the Philistines rule over us? and what is this that thou hast done unto us? And he said unto them, As they did unto me, so have I done unto them.
Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
12 And they said unto him, To bind thee are we come down, to deliver thee into the hand of the Philistines. And Samson said unto them, Swear unto me, that ye will not assail me yourselves.
Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
13 And they said unto him, thus, No; for we will [only] bind thee fast, and deliver thee into their hand; but we will in no-wise kill thee. And they bound him with two new cords, and brought him up from the rock.
Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
14 When he was come unto Lechi, the Philistines shouted against him; but the Spirit of the Lord came suddenly over him, and the cords that were upon his arms became as flax threads that are burnt with fire, and his bands melted from off his hands.
Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
15 And he found a fresh jaw-bone of an ass, and put forth his hand, and took it, and smote therewith a thousand men.
Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
16 And Samson said, With a jaw-bone of an ass, heaps upon heaps, with the jaw-bone of an ass have I smitten a thousand men.
Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
17 And it came to pass, when he had made an end of speaking, that he cast away the jaw-bone out of his hand, and called that place Ramath-lechi.
Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
18 And he became very thirsty, and he called on the Lord, and said, Thou hast granted through the hand of thy servant this great deliverance; and now shall I die for thirst, and fall into the hand of the uncircumcised?
Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
19 But God clave a hollow place that was at Lechi, and there came forth water out of it; and he drank, and his spirit came again, and he revived; wherefore he called the name thereof 'En-hakkore, which is in Lechi unto this day.
Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
20 And he judged Israel in the days of the Philistines twenty years.
Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.