< Judges 1 >

1 And it came to pass after the death of Joshua, that the children of Israel asked the Lord, saying, Who shall go up for us against the Canaanites at the first, to fight against them?
Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
2 And the Lord said, Judah shall go up; behold, I have delivered the land into his hand.
Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
3 And Judah said unto Simeon his brother, Come up with me into my lot, and we will fight against the Canaanites; and I likewise will go with thee into thy lot. So Simeon went with him.
Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
4 And Judah went up; and the Lord delivered the Canaanites and the Perizzites into their hand; and they smote [of] them in Bezek ten thousand men.
Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
5 And they found Adoni-bezek in Bezek; and they fought against him, and they smote the Canaanites and the Perizzites.
A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
6 But Adoni-bezek fled; and they pursued after him, and caught him, and cut off his thumbs and his great toes.
Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
7 And Adoni-bezek said, Seventy kings, having their thumbs and their great toes cut off, gathered food under my table: as I have done, so hath God requited me. And they brought him to Jerusalem, and he died there.
Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
8 And the children of Judah fought against Jerusalem, and captured it, and they smote it with the edge of the sword, and the city they set on fire.
Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
9 And afterward did the children of Judah go down to fight against the Canaanites, that dwelt in the mountain, and in the south, and in the lowlands.
Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
10 And Judah went against the Canaanites that dwelt in Hebron; [now the name of Hebron was formerly Kiryath-arba'; ] and they smote Sheshai, and Achiman, and Talmai.
Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
11 And he went from there against the inhabitants of Debir; and the name of Debir was formerly Kiryath-sepher:
Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
12 And Caleb said, He that will smite Kiryath-sepher, and capture it, to him will I give 'Achsah my daughter for wife.
Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
13 And 'Othniel the son of Kenaz, Caleb's younger brother, captured it: and he gave him 'Achsah his daughter for wife.
Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
14 And it came to pass, when she came to him, that she persuaded him to ask of her father a field: and she alighted from off her ass; and Caleb said unto her, What aileth thee?
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
15 And she said unto him, Give me a blessing; for thou hast given me a dry land: give me also springs of water. And Caleb gave her the upper springs and the nether springs.
Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
16 And the children of the Kenite, the father-in-law of Moses, went up out of the city of palm-trees with the children of Judah into the wilderness of Judah, which is at the south of 'Arad; and they went and dwelt with the people.
Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
17 And Judah went with Simeon his brother, and they smote the Canaanites that inhabited Zephath, and devoted it. And the name of the city was called Chormah.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
18 And Judah captured Gazzah with its territory, and Ashkelon with its territory, and 'Ekron with its territory.
Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
19 And the Lord was with Judah; and he took possession of the mountain; but could not drive out the inhabitants of the valley, because they had chariots of iron.
Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
20 And they gave Hebron unto Caleb, as Moses had spoken; and he drove out thence the three sons of 'Anak.
Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
21 And the Jebusites that inhabited Jerusalem, the children of Benjamin did not drive out; but the Jebusites dwelt with the children of Benjamin in Jerusalem until this day.
Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
22 And the house of Joseph, these also, went up against Beth-el; and the Lord was with them.
To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
23 And the house of Joseph sent to spy out Beth-el: now the name of the city formerly was Luz.
Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
24 And the watchers saw a man coming forth out of the city, and they said unto him, Show us, we pray thee, the entrance into the city, and we will show thee kindness.
’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
25 And he showed them the entrance into the city, and they smote the city with the edge of the sword; but the man and all his family they let go free.
Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
26 And the man went into the land of the Hittites, and built a city, and called its name Luz: this is its name unto this day.
Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
27 Neither did Menasseh drive out [the inhabitants of] Beth-shean and its towns, nor Ta'anach and its towns, nor the inhabitants of Dor and its towns, nor the inhabitants of Yible'am and its towns, nor the inhabitants of Megiddo and its towns; but the Canaanites succeeded to remain in this land.
Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
28 And it came to pass, when Israel became strong, that they put the Canaanites to tribute; but they did not drive them out entirely.
Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
29 Neither did Ephraim drive out the Canaanites that dwelt in Gezer; and the Canaanites dwelt in the midst of them at Gezer.
Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
30 Zebulun did not drive out the inhabitants of Kitron, nor the inhabitants of Nahalol; and the Canaanites dwelt in the midst of them, and became tributary.
Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
31 Asher did not drive out the inhabitants of 'Akko, nor the inhabitants of Zidon, nor of Achlab, nor of Achzib, nor of Chelbah, nor of Aphik, nor of Rechob;
Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
32 And the Asherites dwelt in the midst of the Canaanites, the inhabitants of the land; for they did not drive them out.
kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
33 Naphtali did not drive out the inhabitants of Beth-shemesh, nor the inhabitants of Beth-'anath; and he dwelt in the midst of the Canaanites, the inhabitants of the land; nevertheless the inhabitants of Beth-shemesh and of Beth-anath became tributary unto them.
Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
34 And the Emorites forced the children of Dan into the mountain; for they would not suffer them to come down into the valley;
Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
35 And the Emorites succeeded to remain on mount Cheres, in Ayalon, and in Sha'albim; but when the hand of the house of Joseph prevailed, they became tributary.
Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
36 And the territory of the Emorites was from the ascent of 'Akrabbim, from the Rock upward.
Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.

< Judges 1 >