< Joshua 6 >

1 Now Jericho was shut up, and barred up, because of the children of Israel: no one went out, and no one came in.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 And the Lord said unto Joshua, See, I have given into thy hand Jericho and its king, even the mighty men of valor.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 And ye shall compass the city, all the men of war, going round about the city once. Thus shalt thou do six days.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 And seven priests shall bear before the ark seven cornets of rams' horns; and on the seventh day shall ye compass the city seven times, and the priests shall blow with the cornets.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 And it shall come to pass, that, when they blow a long blast with the ram's horn, when ye hear the sound of the cornet all the people shall utter a great shout; and the wall of the city shall fall down flat, and the people shall ascend up every man straight before him.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 And Joshua the son of Nun called the priests, and said unto them, Take up the ark of the covenant, and let seven priests bear seven cornets of rams' horns before the ark of the Lord.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 And he said unto the people, Pass on, and compass the city, and let the armed men pass on before the ark of the Lord.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 And it came to pass, when Joshua had spoken unto the people, that the seven priests, bearing the seven cornets of rams' horns before the Lord, passed on and blew with the cornets; and the ark of the covenant of the Lord followed them.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 And the armed men went before the priests that blew the cornets, and the rereward came after the ark, going on, and blowing with the cornets.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 And Joshua had commanded the people, saying, Ye shall not shout, nor let your voice be heard, neither shall any word proceed out of your mouth, until the day I bid you, Shout; and then shall ye shout.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 So the ark of the Lord compassed the city, going round it once; and they came into the camp, and lodged in the camp.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 And Joshua rose early in the morning, and the priests took up the ark of the Lord.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 And the seven priests bearing the seven cornets of rams' horns before the ark of the Lord went on continually, and blew with the cornets; and the armed men went before them; and the rereward came after the ark of the Lord, going on, and blowing with the cornets.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 And they compassed the city on the second day once, and returned into the camp: so did they six days.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 And it came to pass on the seventh day, that they rose early about the dawning of the day, and compassed the city after this manner seven times; only on that day they compassed the city seven times.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 And it came to pass at the seventh time, when the priest blew with the cornets, that Joshua' said unto the people, Shout; for the Lord hath given you the city.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 And the city shall be devoted, it, and all that is therein, to the Lord: only Rachab the harlot shall live, she and all that are with her in the house; because she did hide the messengers that we sent.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 But ye, keep yourselves from the devoted things, lest ye devote and yet take of the devoted things, and make the camp of Israel a curse, and trouble it.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 And all the silver, and gold, and vessels of copper and iron, shall be holy unto the Lord: into the treasury of the Lord shall they come.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 So the people shouted, when they blew with the cornets; and it came to pass, when the people heard the sound of the cornet, that the people uttered a great shout, and the wall fell down flat, and the people went up into the city, every man straight before him, and they captured the city.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 And they utterly destroyed all that was in the city, both man and woman, young and old, and ox, and lamb, and ass, with the edge of the sword.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 But unto the two men that had spied out the country, Joshua said, Go into the house of the woman, the harlot, and bring out thence the woman, and all belonging to her, as ye have sworn unto her.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 And the young men, the spies, went in, and brought out Rachab, and her father, and her mother, and her brothers, and all belonging to her: and they brought out all her kindred, and they left them without the camp of Israel.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 And the city they burnt with fire, and all that was therein: only the silver, and the gold, and the vessels of copper and of iron, they put into the treasury of the house of the Lord.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 And Rachab the harlot did Joshua save alive, and her father's household, and all belonging to her; and she dwelt in the midst of Israel even unto this day; because she had hidden the messengers, whom Joshua had sent to spy out Jericho.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 And Joshua adjured [the people] at that time, saying, Cursed be the man before the Lord, that will rise up and build this city Jericho: with his first-born shall he lay its foundation, and with his youngest shall he set up its gates.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 And the Lord was with Joshua; and his fame was spread throughout all the country.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.

< Joshua 6 >