< Joshua 21 >

1 Then came near the heads of the divisions of the Levites unto Elazar the priest, and unto Joshua the son of Nun, and unto the heads of the divisions of the tribes of the children of Israel;
To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
2 And they spoke unto them at Shiloh, in the land of Canaan, saying, The Lord commanded by the hand of Moses to give unto us cities to dwell in, with the open spaces thereof for our cattle.
Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
3 And the children of Israel gave unto the Levites from their inheritance, at the order of the Lord, these cities and their open spaces.
Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
4 And the lot came out for the families of the Kehathites: and the children of Aaron the priest, who were of the Levites, obtained from the tribe of Judah, and from the tribe of Simeon, and from the tribe of Benjamin, by lot, thirteen cities.
Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
5 And the rest of the children of Kehath obtained from the families of the tribe of Ephraim, and from the tribe of Dan, and from the half tribe of Menasseh, by lot, ten cities.
Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
6 And the children of Gershon obtained from the families of the tribe of Issachar, and from the tribe of Asher, and from the tribe of Naphtali, and from the half tribe of Menasseh in Bashan, by lot, thirteen cities.
Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
7 The children of Merari after their families obtained from the tribe of Reuben, and from the tribe of Gad, and from the tribe of Zebulun, twelve cities.
Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
8 And the children of Israel gave unto the Levites these cities with their open spaces, as the Lord had commanded by the hand of Moses, by lot.
Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
9 And they gave from the tribe of the children of Judah, and from the tribe of the children of Simeon, these cities which are called by name.
Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
10 And the children of Aaron, of the families of the Kehathites, of the children of Levi, obtained them; —for they had the first lot.
(ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
11 And they gave unto them Kiryath-arba', [the father of 'Anak, ] which is Hebron, in the mountain of Judah, with the open spaces thereof round about it;
an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
12 But the fields of the city, and its villages, they gave to Caleb the son of Yephunneh for his possession.
Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
13 And to the children of Aaron the priest they gave the city of refuge for the manslayer, Hebron with its open spaces, and Libnah with its open spaces,
Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
14 And Yattir with its open spaces, and Eshtemoa' with its open spaces.
da Yattir, da Eshtemowa,
15 And Cholon with its open spaces, and Debir with its open spaces,
da Holon, da Debir,
16 And 'Ayin with its open spaces, and Yuttah with its open spaces, and Beth-shemesh with its open spaces: nine cities from those two tribes.
da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
17 And from the tribe of Benjamin, Gib'on with its open spaces, Geba' with its open spaces,
Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
18 'Anathoth with its open spaces, and 'Almon with its open spaces: four cities.
Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
19 All the cities of the children of Aaron, the priests, were thirteen cities with their open spaces.
Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
20 And the families of the children of Kehath, the Levites, who remained of the children of Kehath, obtained the cities of their lot from the tribe of Ephraim.
Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
21 And they gave to them the city of refuge for the manslayer, Shechem with its open spaces in the mountain of Ephraim, and Gezer with its open spaces,
A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
22 And Kibzayim with its open spaces, and Beth-choron with its open spaces: four cities.
Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
23 And from the tribe of Dan, Elteke with its open spaces, Gibbethon with its open spaces,
Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
24 Ayalon with its open spaces, Gath-rimmon with its open spaces: four cities.
Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
25 And from the half tribe of Menasseh, Ta'nach with its open spaces, and Gath-rimmon with its open spaces: two cities.
Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
26 All the cities were ten with their open spaces for the families of the children of Kehath that remained.
Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
27 And unto the children of Gershon, of the families of the Levites, [they gave] from the other half tribe of Menasseh the city of refuge for the manslayer, Golan in Bashan with its open spaces, and Be'eshterah with its open spaces: two cities.
Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
28 And from the tribe of Issachar, Kishyon with its open spaces, Daberath with its open spaces,
daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
29 Yarmuth with its open spaces, 'En-gannim with its open spaces: four cities.
Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
30 And from the tribe of Asher, Mishal with its open spaces, Abdon with its open spaces.
daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
31 Chelkath with its open spaces, and Rechob with its open spaces: four cities.
Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
32 And from the tribe of Naphtali, the city of refuge for the manslayer, Kedesh in Galilee with its open spaces, and Chammothdor with its open spaces, and Karthan with its open spaces: three cities.
daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
33 All the cities of the Gershunites according to their families were thirteen cities with their open spaces.
Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
34 And unto the families of the children of Merari, the remainder of the Levites, [they gave] from the tribe of Zebulun, Yokne'am with its open spaces, and Karthah with its open spaces,
Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
35 Dimnah with its open spaces, Nahalal with its open spaces: four cities.
Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
38 And from the tribe of Gad, the city of refuge for the manslayer, Ramoth in Gil'ad with its open spaces, and Machanayim with its open spaces,
daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
39 Cheshbon with its open spaces, Ya'zer with its open spaces: four cities in all.
Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
40 All the cities for the children of Merari after their families, they who were remaining of the families of the Levites, even their lot was twelve cities.
Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
41 All the cities of the Levites in the midst of the possession of the children of Israel were forty and eight cities with their open spaces.
Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
42 These cities were every one with their open spaces round about them: thus it was with all these cities.
Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
43 And the Lord gave unto Israel all the land which he had sworn to give unto their fathers; and they possessed it, and dwelt therein.
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
44 And the Lord gave them rest round about, all just as he had sworn unto their fathers: and there stood not up before them a man of all their enemies; all their enemies the Lord delivered into their hand.
Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
45 There failed not aught of all the good thing which the Lord had spoken unto the house of Israel: it all came to pass.
Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.

< Joshua 21 >