< Joshua 2 >

1 And Joshua, the son of Nun, had sent out from Shittim two men as spies, secretly, saying, Go ye, view the land and especially Jericho; and they went, and came unto the house of a woman, a harlot, whose name was Rachab, and they lodged there.
Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
2 And it was told unto the king of Jericho, saying, Behold, men came in hither this night, of the children of Israel, to search out the country.
Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
3 And the king of Jericho sent to Rachab, saying, Bring forth the men who are come to thee, who came to thy house; for, to search out all the country are they come.
Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
4 But the woman had taken the two men, and hidden them; and she said, It is true, the men came unto me, but I knew not whence they were.
Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
5 And it came to pass, about the time of shutting the gate, when it was dark, that the men went out; I know not whither the men are gone: pursue quickly after them, for ye can overtake them.
da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
6 But she had brought them up to the roof, and had hidden them among the stalks of flax, which she had laid in order upon the roof.
(Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
7 And the men pursued after them, by the way to the Jordan unto the fords; and the gate was closed, as soon as those who pursued after them were gone out.
Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
8 But they had not yet laid themselves down, when she came up unto them upon the roof.
Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
9 And she said unto them, I know that the Lord hath given you the land, and that the terror of you hath fallen upon us, and that all the inhabitants of the land are become faint-hearted, because of you.
ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
10 For we have heard, how that the Lord dried up the waters of the Red Sea before you, when ye went forth out of Egypt; and what ye have done unto the two kings of the Emorites, who were on the other side of the Jordan, unto Sichon and 'Og, whom ye have utterly destroyed.
Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
11 And when we heard this, our heart melted, and there remained not any more courage in any man, because of you; for the Lord your God is alone God in the heavens above, and upon the earth beneath.
Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
12 And now swear, I pray you, unto me by the Lord, because I have shown you kindness, that ye will also, for your part, show kindness, unto my father's house; and give me a sure token,
Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
13 That ye will preserve the life of my father, and my mother, and my brothers, and my sisters, and all that they have, and deliver our lives from death.
za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
14 And the men said unto her, Our life shall be [doomed] to death instead of yours, if ye tell not this our business; and it shall be, when the Lord giveth us the land, that we will show thee kindness and truth.
Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
15 Then she let them down by a cord through the window; for her house was within the town wall, and within the wall she dwelt.
Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
16 And she said unto them, Get you to the mountain, lest the pursuers meet with you; and hide yourselves there three days, until the pursuers be returned; and afterward ye may go your way.
Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
17 And the men said unto her, We will be blameless of this thy oath which thou hast caused us to swear.
Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
18 Behold, when we come into the land, this line of scarlet thread shalt thou bind in the window by which thou hast let us down; and thy father, and thy mother, and thy brothers, and all thy father's household, thou must bring together unto thee into the house.
sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
19 And it shall be, that whosoever will go out of the doors of thy house into the street, his blood shall be upon his head, and we will be guiltless; and whosoever will remain with thee in the house, his blood shall be on our head, if a hand be laid upon him.
In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
20 And if thou tell this our business, then will we be free of thy oath which thou hast caused us to swear.
In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
21 And she said, According unto your words, so be it; and she dismissed them, and they departed; and she bound the scarlet line in the window.
Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
22 And they went, and came unto the mountain, and they remained there three days, until the pursuers were returned; and the pursuers sought throughout all the way, but found nothing.
Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
23 And the two men returned, and descended from the mountain, and passed over, and came to Joshua the son of Nun, and related to him all the things that had befallen them.
Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
24 And they said unto Joshua, Truly the Lord hath given up into our hand all the country; for all the inhabitants of the country are already become faint-hearted because of us.
Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”

< Joshua 2 >