< Joshua 19 >
1 And then came forth the second lot for Simeon, for the tribe of the children of Simeon according to their families; and their inheritance was within the inheritance of the children of Judah.
Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
2 And they obtained in their inheritance Beer-sheba', [or] Sheba', and Moladah,
Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
3 And Chazar-shu'al, and Balah, and 'Ezem,
Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
4 And Eltolad, and Bethul, and Chormah,
Eltolad, Betul, Horma,
5 And Ziklag, and Beth-hamarcaboth, and Chazar-sussah,
Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
6 And Beth-lebaoth, and Sharuchen: thirteen cities and their villages.
Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
7 'Ayin, Rimmon, and 'Ether, and 'Ashan; four cities and their villages.
Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
8 And all the villages that were round about these cities up to Ba'alath-beer, South Ramah. This is the inheritance of the tribe of the children of Simeon according to their families.
da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
9 Out of the portion of the children of Judah was the inheritance of the children of Simeon; for the portion of the children of Judah was too much for them; therefore the children of Simeon obtained their inheritance within their inheritance.
Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
10 And then came up the third lot for the children of Zebulun according to their families; and the boundary of their inheritance extended up to Sarid;
Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
11 And their boundary went up toward the sea, and Mar'alah, and touched on Dabbesheth, and touched on the brook that is before Yokne'am;
Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
12 And turned from Sarid eastward toward the rising of the sun unto the border of Kisloth-tabor, and then went out to Daberath, and went up to Yaphia';
Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
13 And from there it passed on in front to the east unto Gath-Chepher, to 'Eth-kazin, and went out to Rimmon, whence it extended to Ne'ah;
Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
14 And this boundary turned about on the north side to Channathon; and its terminations were in the valley of Yiph-thach-el;
A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
15 And Kattath, and Nahallal, and Shimron, and Yidalah, and Beth-lechem: twelve cities with their villages.
Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
16 This is the inheritance of the children of Zebulun according to their families, these cities with their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
17 For Issachar came out the fourth lot, for the children of Issachar according to their families.
Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
18 And their boundary went to Yizre'el, and Kessulloth, and Shunem,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
19 And Chapharayim, and Shion, and Anacharath,
Hafarayim, Anaharat,
20 And Rabbith, and Kishyon, and Abez,
Rabbat, Kishiyon, Ebez,
21 And Remeth, and 'En-gannim, and 'En-chaddah, and Beth-pazazz;
Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
22 And the boundary touched on Tabor, and Shachazimah, and Beth-shemesh; and the terminations of their boundaries were at the Jordan: sixteen cities with their villages.
Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
23 This is the inheritance of the tribe of the children of Issachar according to their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
24 And then came out the fifth lot for the tribe of the children of Asher according to their families.
Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
25 And their boundary was Chelkath, and Chali, and Beten, and Achshaph,
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26 And Allammelech, and 'Am'ad, and Mishal; and it touched on Carmel at the sea, and on Shichor-libnath;
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27 And it turned toward the rising of the sun to Beth-dagon, and touched on Zebulun, and on the valley of Yiphthach-el at the north, on Beth-ha'emek, and Ne'iel, and went out to Cabul on the left,
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28 And 'Ebron, and Rechob, and Chammon, and Kanah, up to Zidon the great city,
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29 And then the boundary turned back to Ramah, and to the city of Mibzar-zor; and then the boundary turned back to Chossah; and the terminations were by the sea in the district toward Achzib;
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30 And 'Ummah and Aphek, and Rechob: twenty and two cities with their villages.
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
31 This is the inheritance of the tribe of the children of Asher according to their families, these cities with their villages.
Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
32 Unto the children of Naphtali came out the sixth lot, for the children of Naphtali according to their families.
Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
33 And their boundary was from Cheleph, from Allon-beza-'anannim, and Adami-hanekeb, and Yabneel, as far as Lakkum; and its terminations were at the Jordan;
Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
34 And then the boundary turned westward to Aznoth-tabor, and went out from there to Chukkok, and touched on Zebulun on the south, and touched on Asher on the west, and on Judah upon the Jordan toward the rising of the sun.
Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
35 And fortified cities, Ziddim, Zer, and Chammath, Rakkath, and Kinnereth,
Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
36 And Adamah, and Ramah, and Chazor,
Adama, Rama, Hazor,
37 And Kedesh, and Edre'i, and 'En-chazor,
Kedesh, Edireyi, En Hazor,
38 And Yiron, and Migdal-el, Chorem, and Beth-'anath, and Beth-shemesh: nineteen cities with their villages.
Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
39 This is the inheritance of the tribe of the children of Naphtali according to their families, the cities and their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
40 For the tribe of the children of Dan according to their families came out of the seventh lot.
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41 And the boundary of their inheritance was Zor'ah, and Eshtaol, and 'Ir-shemesh,
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42 And Sha'alabbin, and Ayalon, and Yithlah,
Shalim, Aiyalon, Itla,
43 And Elon, and Thimnathah, and 'Ekron,
Elon, Timna, Ekron,
44 And Eltekeh, and Gibbethon, and Ba'alath,
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45 And Yehud, and Bene-berak, and Gathrimmon.
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46 And Me-hayarkon, and Rakkon, with the boundary before Yapho.
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47 And the territory of the children of Dan went out beyond these; for the children of Dan went up and fought against Leshem, and captured it, and smote it with the edge of the sword, and took possession of it, and dwelt therein, and they called Leshem, Dan, after the name of Dan their father.
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48 This is the inheritance of the tribe of the children of Dan according to their families, these cities with their villages.
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
49 And they made an end of dividing the land for inheritance after its boundaries; and the children of Israel gave an inheritance to Joshua the son of Nun among them;
Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
50 By the order of the Lord did they give him the city which he had asked, Timnathserach on the mountain of Ephraim: and he built the city, and dwelt therein.
yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
51 These are the inheritances, which Elazar the priest, and Joshua the son of Nun, and the heads of the divisions of the tribes of the children of Israel, divided for an inheritance by lot, at Shiloh before the Lord, at the door of the tabernacle of the congregation. So they made an end of dividing the country.
Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.