< Joshua 14 >
1 And these are the countries which the children of Israel obtained as an inheritance in the land of Canaan, which Elazar the priest, and Joshua the son of Nun, and the heads of the divisions of the tribes of the children of Israel, distributed for an inheritance unto them,
Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
2 By the lot as their inheritance: as the Lord had commanded by the hand of Moses, for the nine tribes, and the half tribe.
Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
3 For Moses had given the inheritance of the two tribes and the half tribe on the other side of the Jordan; but unto the Levites he had given no inheritance among them.
Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
4 For the children of Joseph were two tribes, Menasseh and Ephraim; therefore they gave no portion unto the Levites in the land, save cities to dwell in, with their open spaces for their cattle and for their substance.
gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
5 As the Lord had commanded Moses, so did the children of Israel, and so divided they the land.
Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 And the children of Judah came near unto Joshua in Gilgal; and Caleb the son of Yephunneh the Kenizzite said unto him, Thou well knowest the word which the Lord spoke unto Moses the man of God concerning me and thyself in Kadesh-barnea'.
Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
7 Forty years old was I when Moses the servant of the Lord sent me from Kadesh-barnea' to spy out the land; and I brought him word again as it was in my heart.
Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
8 But my brethren who had gone up with me caused the heart of the people to be faint; but I wholly followed the Lord my God.
amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
9 And Moses swore on that day, saying, Surely the land whereon thy foot hath trodden shall belong to thee for an inheritance, and to thy children for ever; because thou hast wholly followed the Lord my God.
Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
10 And now, behold, the Lord hath kept me alive, as he hath spoken: it is now forty and five years since the Lord spoke this word unto Moses, while Israel wandered in the wilderness; and now, behold, I am this day eighty and five years old.
“Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
11 I am yet this day as strong as I was on the day that Moses sent me: as my strength was then, even so is my strength now, for war, and to go out, and to come in.
Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
12 Now therefore give me this mountain, whereof the Lord spoke on that day; for thou didst hear on that day that the 'Anakim were there, and great fortified cities: perhaps the Lord will be with me, and I shall drive them out, as the Lord hath spoken.
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
13 And Joshua blessed him, and gave Hebron unto Caleb the son of Yephunneh for an inheritance.
Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
14 Therefore did Hebron become the inheritance of Caleb the son of Yephunneh the Kenizzite unto this day; for the cause that he had wholly followed the Lord the God of Israel.
Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
15 And the name of Hebron was aforetimes Kiryatharba', who was the greatest man among the 'Anakim. And the land had rest from war.
(Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.