< Jonah 1 >

1 The word of the Lord also came unto Jonah the son of 'Amitthai, saying,
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 Arise, Go unto Nineveh, the great city, and proclaim against her; for their wickedness is come up before me.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 But Jonah rose up to flee unto Tharshish from the presence of the Lord; and he went down to Joppa, and found a ship going to Tharshish, and paid the fare thereof, and went down into it, to go with them unto Tharshish, from the presence of the Lord.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 But the Lord excited a great wind upon the sea, and there was a mighty tempest on the sea; and it was thought that the ship would be broken in pieces.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 And the mariners were afraid, and called every man unto his god; and they cast forth the articles which were in the ship into the sea, to be lightened of them. But Jonah was gone down into the hold of the ship, and lay down, and was fast asleep.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 So the ship-master came near unto him, and said unto him, Why dost thou sleep? arise, call upon thy God: perhaps it be that God will think of us, that we may not be lost.
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 And they said one to the other, Come, and let us cast lots; that we may know for whose cause this evil hath happened unto us. And they cast lots, and the lot fell upon Jonah.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Then said they unto him, Tell us, we pray thee, thou for whose cause this evil hath happened unto us, What is thy business? and whence comest thou? what is thy country? and of what people art thou?
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 And he said unto them, I am a Hebrew; and I fear the Lord, the God of heaven, who hath made the sea and the dry land.
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Then were the men exceedingly afraid and they said unto him, What is this thou hast done? for the men knew that he was flying from the presence of the Lord; because he had told them.
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 And they said unto him, What shall we do unto thee, that the sea may become calm around us? for the sea grew more and more tempestuous.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 And he said unto them, Take me up, and cast me forth into the sea: so shall the sea be calm around you; for I know well that because of me is this great tempest upon you.
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 Nevertheless the men rowed hard to bring [the ship] back to the land; but they could not; for the sea grew more and more tempestuous around them.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 And they called unto the Lord, and said, We beseech thee, O Lord, let us not be lost, we pray thee, for the life of this man, and lay not upon us [the guilt of] innocent blood; for thou art the Lord, as it pleaseth thee so dost thou do.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 And they took up Jonah, and cast him forth into the sea: and the sea ceased from its raging.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 And the men feared the Lord very greatly; and they offered a sacrifice unto the Lord, and made vows.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 And the Lord made ready a large fish to swallow up Jonah: and Jonah was in the belly of the fish three days and three nights.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.

< Jonah 1 >