< Joel 3 >

1 For, behold, in those days, and in that time, when I will cause to return the captivity of Judah and Jerusalem,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 Then will I assemble all the nations, and I will bring them down into the valley of Jehoshaphat, and I will hold judgment with them there because of my people and my heritage Israel, whom they have scattered among the nations, and for my land [which] they have divided out.
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 And for my people did they cast lots; and gave a boy for a harlot, and sold a girl for wine, and drank it.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 And also ye, what have ye to do with me, O Tyre, and Zidon, and all ye districts of Philistia? is this the recompense which ye repay me? or do ye only commence to render me evil?— swiftly and speedily will I bring back your recompense upon your own head;
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 Because my silver and my gold have ye taken, and the handsomest of my precious things have ye carried into your temples;
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 And the children of Judah and the children of Jerusalem have ye sold unto the sons of the Jevanim, in order to remove them far from their borders.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Behold, I will awaken them out of the place whither ye have sold them, and I will bring back your recompense upon your own head;
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 And I will deliver your sons and your daughters into the hand of the children of Judah, and they shall sell them to the Sabeans, to a nation far off; for the Lord hath spoken it.
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Proclaim ye this among the nations, Prepare war, wake up the mighty men; let them draw near; let them come up—all the men of war.
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Beat your plough-shares into swords, and your pruning-knives into spears: let the weak say, I am a hero.
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Assemble hastily together, and come, all ye nations from every side, and gather yourselves together: there doth the Lord strike down thy mighty ones.
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 Let the nations awake, and come up to the valley of Jehoshaphat; for there will I sit to judge all the nations from every side.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Put forth the sickle; for the harvest is ripe: come, tread down [the grapes]; for the press is full; the vats overflow; for great is their wickedness.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Multitudes, multitudes are in the valley of decision; for near is the day of the Lord in the valley of decision.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 Sun and moon are obscured, and stars withdraw their brightness.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 And the Lord will cry aloud out of Zion, and from Jerusalem will he send forth his voice; and the heavens and the earth shall quake; but the Lord will be a refuge for his people, and a stronghold for the children of Israel.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 So shall ye know that I am the Lord your God, dwelling on Zion, my holy mount: and Jerusalem shall be holy, and strangers shall not pass through her any more.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 And it came to pass on that day, that the mountains shall drop down sweet new wine, and the hills shall flow with milk, and all the ravines of Judah shall flow with water; and a spring shall come forth out of the house of the Lord, and shall water the valley of Shittim.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 Egypt shall become a desolate land, and Edom shall become a desolate wilderness; because of the violence against the children of Judah, in whose land they have shed innocent blood.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 But Judah shall be inhabited for ever, and Jerusalem from generation to generation.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 And I will avenge their blood that I have not yet avenged; for the Lord dwelleth in Zion.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Joel 3 >