< Joel 1 >

1 The word of the Lord that came to Joel the son of Pethuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Hear this, ye old men, and give ear, all ye inhabitants of the land. Did ever such a thing as this come to pass in your days, or ever in the days of your fathers?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Tell ye of it to your children, and let your children tell it to their children, and their children to another generation.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 What the caterpillar left hath the locust eaten; and what the locust left hath the cankerworm eaten; and that which the cankerworm left hath the cricket eaten.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Wake up, ye drunkards, and weep; and wail, all ye drinkers of wine, because of the sweet new wine, that it is taken away from your mouth.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 For a nation is come up over my land, strong, and without number; its teeth are the teeth of a lion, and it hath the cutting-teeth of the lioness.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 It hath laid my vine waste, and barked my fig-tree: it hath peeled it clean bare, and cast it down; made white are its light branches.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Lament like a virgin girded with sackcloth for the betrothed of her youth.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Cut off are the meat-offering and the drink-offering from the house of the Lord: now mourn the priests, the ministers of the Lord.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Wasted is the field, the land mourneth; for wasted is the corn: dried up is the new wine, withered is the oil.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Be ashamed, O ye husbandmen; wail, O ye vinedressers, for the wheat and for the barley; because lost is the harvest of the field.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 The vine is made ashamed, and the fig-tree is withered; the pomegranate-tree, the palm-tree also, and the apple-tree, even all the trees of the field, are dried up; because joy hath ceased from the children of men.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Gird yourselves [with sackcloth], and lament, ye priests; wail, ye ministers of the altar: come, remain all night in sackcloth, ye ministers of my God; for there are withholden from the house of your God the meat-offering and the drink-offering.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Sanctify ye a fast, proclaim a solemn assembly, gather the elders, all the inhabitants of the land, into the house of the Lord your God, and cry aloud unto the Lord.
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Alas for the day! for the day of the Lord is at hand, and like destruction from the Almighty will it come.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Is not before our eyes the food cut off, from the house of our God joy and gladness?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 The grains of seed are rotten under their clods, laid desolate are the garners, pulled down are the barns; for the corn is dried up.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 How do the beasts groan! how do the herds of cattle roam about; because there is no pasture for them: yea, the flocks of sheep are made to perish.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 To thee O Lord, will I cry; for the fire hath devoured the pastures of the wilderness, and the flame hath singed all the trees of the field.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Also the beasts of the field cry unto thee panting; for the brooks of waters are dried up, and a fire hath devoured the pastures of the wilderness.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joel 1 >