< Job 38 >

1 Then did the Lord address Job out of the storm-wind, and said,
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Who is this that casteth darkness [on my] counsel by words without knowledge?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Do but gird up like a mighty man thy loins: and I will ask thee, and do thou inform me.
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Where wast thou when I laid the foundations of the earth? tell it, if thou hast any understanding [of it].
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Who fixed her measurements, if thou knowest it? or who stretched the measuring-line over her?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Upon what are her foundation-pillars placed at rest? or who laid her corner-stone:
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 When altogether sang the morning stars in gladness, and shouted for joy all the sons of God?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 And who closed up with doors the sea, when, issuing forth, it came out of the deep bosom of the earth?
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 When I made the clouds its garment, and thick fog its swaddling-cloth,
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 And when I decreed for it my law, and set [for it] bars and doors,
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 And said, Thus far mayest thou come, but no farther; and here shall be stayed [thy strength] in the pride of thy waves?
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Didst thou ever, in all thy days, command the morning; didst thou ever assign the morning-dawn its place:
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 That it might lay hold of the ends of the earth, so that the wicked might be shaken out therefrom?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 She is changed as the sealing-clay: and [all things] stand as though newly clad.
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 And from the wicked is their light withdrawn, and the high-raised arm is broken.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Didst thou ever penetrate as far as the springs of the sea? or wander through the bottom of the deep?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Were the gates of death ever laid open unto thee? or canst thou see the doors of the shadow of death?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Hast thou a clear understanding of the breadth of the earth? Tell it, if thou knowest it all.
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Where is the way [to the spot where] the light dwelleth? and the darkness—where is its place,
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 That thou mightest take each to its boundary, and that thou mightest mark the pathways to its house?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Thou [surely] knowest it; because thou wast then born, and the number of thy days is great!
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Didst thou ever enter into the treasuries of the snow? or canst thou see the treasuries of the hail,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Which I have reserved for the time of distress, for the day of fight and battle?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Where is the way [to the spot where] the light divideth itself, [where] the east wind is scattered over the earth?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Who hath divided off watercourses for the overflowing rain, and a way for the lightning [that is followed by] thunders,
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 To bring rain on a land, void of men; on a wilderness wherein no son of earth [is found];
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 To satisfy waste and desolate lands; and to promote the growth of the tender grass?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Hath the rain a father? or who hath begotten the drops of the dew?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Out of whose womb cometh forth the ice? and the hoary frost of heaven—who giveth birth to it?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 [When] like a stone the waters are congealed, and the face of the deep is bound in fetters?
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Canst thou bind together the chains of the Pleiades, or loosen the bands of Orion?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Canst thou bring forth the constellations of the zodiac, each in its season? or canst thou guide the Bear with its young?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Knowest thou the laws of heaven? or dost thou appoint its rule on the earth?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Canst thou lift up to the clouds thy voice, that the abundance of waters may cover thee?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Canst thou send out lightnings, that they may go, and say unto thee, Here are we?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Who hath put wisdom in the dark clouds? or who hath given understanding to the bright meteors?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Who ordaineth the skies with wisdom? or who emptieth out the bottles of heaven.
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 When the dust is poured out as molten metal, and the clods are made to cleave fast together?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Dost thou hunt for the lioness her prey? and suppliest thou the food for the young lions,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 When they are couched in their lairs, rest in the thicket, lying in wait?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Who provideth for the raven his provision? when his young ones cry unto God, and wander about for lack of food?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?

< Job 38 >