< Job 35 >

1 Then commenced Elihu, and said,
Sai Elihu ya ce,
2 Dost thou deem this to be just, that thou hast said, “My righteousness is more than God's?”
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 For thou sayest, “What benefit will it be unto thee? what more profit shall I have, than if I had sinned?”
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 I will truly reply unto thee with words, and unto thy friends with thee.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Look unto the heavens, and see; and gaze on the skies which are higher than thou.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 If thou sin, what dost thou effect against him? and if thy transgressions be multiplied, what canst thou do unto him?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 If thou be righteous, what givest thou him? or what doth he accept out of thy hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 A man like thyself thy wickedness may reach, and a son of earth thy righteousness.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 By reason of the multitude of oppressions [the wicked] cause men to cry: these complain aloud because of the arm of the mighty.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 But [man] saith not, Where is God my maker, who bestoweth joyful songs even in the night;
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Who teacheth us more than the beasts of the earth, and maketh us wiser than the fowls of the heavens?
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There do they cry, but he answereth not: because of the pride of evil men.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Only what is false will God not hear, nor will the Almighty regard it.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Although thou sayest, thou canst not see him: yet the decision is before him; and do thou wait for him.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 But now, because his anger hath punished nothing, shall he not greatly take cognizance of the multitude of sins?
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 But Job openeth wide his mouth for nought: without knowledge he heapeth up words.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”

< Job 35 >