< Job 21 >

1 Then answered Job, and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hear, O hear my speech, and let this be wherewith you give consolations.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Bear with me that I may indeed speak: and after my speaking, then canst thou mock.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 As for me, —is against man my complaint? and if this be so, why should my spirit not be impatient?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Turn yourselves unto me, and be astounded, and lay your hand upon your mouth.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Yea, when I think of it, I am terrified, and shuddering seizeth hold of my flesh.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Wherefore do the wicked live, become old, yea, grow strong in power?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Their seed is firmly established in their presence with them. their offspring are before their eyes.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses are at peace without any dread, and no rod of God [cometh] over them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 The bull of each one gendereth, and disappointeth not: the cow of each one calveth, and casteth not her young.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 They send forth their little ones like a flock, and their children skip about [with joy].
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They sing to the timbrel and harp, and rejoice at the sound of the pipe.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 They wear out their days in happiness, and in a moment they go down to the nether world. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 And yet they say unto God, “Depart from us; and the knowledge of thy ways we desire not.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 What is the Almighty, that we should serve him? and what profit shall we have, if we entreat him urgently?”
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Lo, not in their hand doth their happiness rest! The counsel of the wicked be [still] far from me.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How often is the lamp of the wicked quenched? and how often cometh over them their calamity? and doth [God] distribute their lot in his anger?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Are they as straw before the wind, and as chaff which the stealeth away?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Should God lay up for his children his wrong-doing? it were better that he reward him, that he might know it himself.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 His own eyes ought to see his downfall, and from the wrath of the Almighty ought he to drink.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what care hath he for his household after him, when the number of his months is all apportioned to him?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Is this fitting God, who teacheth knowledge? him who judgeth those that are highest?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 That this one dieth in his full strength, being wholly at ease and quiet;
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His vessels being full of healthy fluid, and the marrow of his bones being well moistened:
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 While this other dieth with an embittered soul, and hath never partaken of any happiness;
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 [And yet] together they must lie down in the dust, and the worms will cover them?
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Behold, I know your thoughts, and the opinions which ye wrongfully devise against me.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For ye say, Where is the house of the noble-minded? and where is the tent of the dwelling-places of the wicked?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Have ye not asked the wayfarers? surely their token ye cannot disregard,
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 That the bad man is reserved for the day of calamity, [that the wicked] are carried forward to the day of wrath.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 [But] who will tell him to his face of his way? and who will repay him what he hath done?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Yea he will indeed be carried to the grave, and men will quickly think of his monument:
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Sweet are to him the clods of the valley; and after him succeedeth every man, as those that were before him are without number.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 How then will ye comfort me with vanity? and of your answers there remaineth only deception.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >