< Job 20 >

1 Then answered Zophar the Na'amathite, and said,
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Even therefore do my inmost thoughts give me an answer, and for this reason do I feel a strong excitement within me.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 Reproof which casteth shame on me must I hear; yet out of my understanding will the spirit give me an answer.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Dost thou know this? from the very beginning of things, from the very time when man was placed upon earth it was,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 That the triumphal shouting of the wicked is ever of but a recent date, and the joy of the hypocrite endureth only for a moment.
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Though his exaltation should mount up to the heavens, and his head should reach unto the clouds;
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Yet when he but turneth round will he vanish for ever; those who have seen him will say, Where is he?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Like a dream will he fly away, and men will find him no more; yea, he will be chased away like a vision of the night.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 If an eye have surveyed him, it will not do so again, and it will not behold him any more in his place.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 His children will suffer oppression from the indigent, and his hands will have to restore his [ill-gotten] wealth.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 [Now] his bones are full of his youthful vigor; but it will [suddenly] lie down with him in the dust.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 If the evil be sweet in his mouth, he will conceal it under his tongue;
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 He will cherish it, and not forsake it; and hold it back within his palate;
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 His food is thus changed within his bowels, and becometh the venom of asps within him.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 The wealth which he hath swallowed, will he have to vomit up again; God will drive it out of his belly.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 The poison of asps will he have to suck; the viper's tongue will slay him.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 He shall not look with pleasure on streams, on flowing brooks of honey and cream.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 He restoreth what he hath labored for, and will not swallow it down; however much he may have obtained by toil, he will not have any joy of it.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Because he oppressed and forsook the indigent; because he took violently away a house, shall he not rebuild it;
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Because he knew not quietness in his bosom, shall he not escape through what is the most precious to him.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Nothing was spared from his craving to eat: therefore shall his wealth not prosper.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 In the fulness of his abundance will distress assail him: every hand of [those he] troubled will come against him.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 In order to fill his belly, [God] will send out against him the fury of his wrath, and will rain it upon him for his eating.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 If he flee from the iron weapon, the brazen bow will strike him through.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 He draweth it, and it cometh out of the body; yea, out of his gall the glittering [arrow] cometh forth: over him come the terrors [of death].
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Entire darkness is laid by for his treasures: a fire not urged by blowing will consume him; it will destroy any one that is left in his tent.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 The heavens will lay open his iniquity; and the earth will raise herself up against him.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 The product of his house will be banished, flowing away on the day of his wrath.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 This is the portion of a wicked man from God, and his decreed heritage from God.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >