< Job 17 >

1 My spirit is broken, my days are cut short, the grave is ready for me.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Yet truly those that mock are with me, and on their offendings must my eye rest.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 And thou, [Creator!] attend, I pray thee, be my surety with thyself: who else is there that would strike hands with me?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 For thou hast concealed their heart against intelligence: therefore art thou not exalted [through them].
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 Every one of them speaketh deceptively to his friends: may also the eyes of his children fail.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 And he hath placed me here as a by-word unto nations; and I become openly as a place of abomination.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 Therefore is my eye dim from vexation, and my limbs are all of them like a shadow.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Upright men must be astonished at this, and the innocent must arouse himself against the hypocrite.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 Yet will the righteous hold firmly on to his way; and he that is clean of hands will acquire additional strength.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 But all of you, do only return, and come but [to me]: and yet I shall not find among you one wise man.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 My days are past, my resolves are broken off, [even the thoughts]—the possessions of my heart.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 These would change the night into day, the light as near in the presence of darkness.—
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 When I hope for the nether world as my house; in the darkness have I spread my couch; (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 When I call to corruption, Thou art my father: Thou art my mother, and my sister, to the worms.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 Ay, where is then my hope? as for my hope, who will see it [fulfilled]?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 Let then my limbs sink down to the nether world: truly in the dust alone there is rest for all. (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >