< Job 11 >
1 Then answered Zophar the Na'amathite, and said.
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Shall a multitude of words not be answered? and is it so that a man full of talk shall be deemed in the right?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Thy inventions are to bring men to silence; and when thou utterest thy mocking no one is to cause thee to feel abashed!
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 For thou hast said [to God], My doctrine is pure, and I am become clean in thy eyes.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 But oh that God would but speak, and open his lips against thee;
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 And that he would declare unto thee the secrets of wisdom; for it is double to that which is really in our possession: and thou wouldst experience that God overlooketh unto thee much of thy iniquity.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Canst thou find out the experience of God? or canst thou find [the way] unto the utmost limit of the Almighty?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 It is as high as heaven; what canst thou effect? it is deeper than the nether world; what canst thou know? (Sheol )
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
9 Longer than the earth is its measure, and broader than the sea.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 If he pass by, and surrender [one to suffering], and call together an assembly, who can hinder him?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 For he knoweth the men of vanity: he seeth the wrong-doer and him who considereth not;
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 And the heartless who acquireth intelligence, and him who is [like] the colt of the wild ass who is transformed into a man.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 If thou truly direct [aright] thy heart, and spread out thy hands toward him: —
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 If wrong be in thy hand, put it far away, and let not wickedness dwell in thy tents.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 For then canst thou lift up thy face free from blemish: yea, thou wilt stand steadfast, and needest not to fear;
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Because thou wilt truly forget thy trouble, and as a waterflood that is passed away wilt thou remember it;
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 And brighter than the noon of day will thy earthly existence arise; and thy obscurity will be like thy morning.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 And thou wilt feel trust, because there is hope: yea, thou wilt search about carefully, and thou wilt lie down in safety.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Also thou wilt stretch thyself out [to rest], with none to make thee afraid; and many will entreat thy favor.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 But the eyes of the wicked shall fail, and the means of escape will vanish from them, and their [sole] hope shall be the breathing out of their soul.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”