< Jeremiah 7 >
1 The word that came to Jeremiah from the Lord, saying,
Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
2 Place thyself in the gate of the house of the Lord, and proclaim there this word, and say, Hear the word of the Lord, all ye of Judah, that enter in by these gates to bow down before the Lord.
“Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
3 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Amend your ways and your deeds, and I will permit you to dwell in this place.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
4 [But] do not rely on the words of falsehood, saying, The temple of the Lord, The temple of the Lord, The temple of the Lord, [as] they [say].
Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
5 For if ye thoroughly amend your ways and your deeds; if ye thoroughly execute justice between a man and his neighbor;
In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
6 If ye oppress not the stranger, the fatherless, and the widow, and shed not innocent blood in this place, and walk not after other gods to your own hurt:
in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
7 Then will I permit you to dwell in this place, in the land that I have given to your fathers, from eternity to eternity.
to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
8 Behold, ye rely on the words of falsehood, that cannot profit.
Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
9 How? will ye steal, murder, and commit adultery, and swear falsely, and burn incense unto Ba'al, and walk after other gods of which ye have no knowledge;
“‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
10 And [then] come and stand before my presence in this house, which is called by my name, and say, “We are delivered;” in order to do all these abominations?
sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
11 Is then this house, which is called by my name, become a den of robbers in your eyes? [But] I also, behold, I have seen it, saith the Lord.
Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
12 For go ye now unto my place which was in Shiloh, where I caused my name to dwell at the first, and see what I did unto it because of the wickedness of my people Israel.
“‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
13 And now, whereas ye have done all these acts, saith the Lord, and I spoke unto you, causing [the prophets] to rise up early and speaking, while ye would not hear; and I called you, but ye would not answer:
Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
14 Therefore will I do unto this house, which is called by my name, whereon ye rely, and unto the place which I have given to you and to your fathers, as I have done to Shiloh.
Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
15 And I will cast you out of my presence, as I have cast out all your brethren, all the seed of Ephraim.
Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
16 But thou—pray not thou in behalf of this people, nor lift up in their behalf entreaty or prayer, nor make intercession to me; for I will not hear thee.
“Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
17 Dost thou not see what they are doing in the cities of Judah and in the streets of Jerusalem?
Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
18 The children gather wood, and the fathers kindle the fire, and the women knead dough, to make cakes for the queen of heaven, and they pour out drink-offerings unto other gods, in order to provoke me to anger.
Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
19 Do they provoke me to anger? saith the Lord, [and] not themselves, to the shame of their own faces?
Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
20 Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold my anger and my fury shall be poured out upon this place, over man, and over beast, and over the trees of the field, and over the fruit of the ground; and it shall burn, and it shall not be quenched.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
21 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Add your burnt-offerings unto your peace-sacrifices, and eat the flesh thereof.
“‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
22 For I spoke not with your fathers, and I commanded them not on the day of my bringing them out of the land of Egypt, concerning burnt-offering or sacrifice;
Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
23 But this thing did I command them, saying, Hearken to my voice, and I will be unto you for a God, and ye shall be unto me for a people; and walk ye altogether on the way which I may command you, in order that it may be well unto you.
amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
24 Yet they hearkened not, and inclined not their ear; but they walked in the counsels, in the stubbornness of their evil heart; and they went backward, and not forward:
Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
25 Since the day that your fathers came forth out of the land of Egypt until this day; and I sent unto you all my servants the prophets, sending them daily in the morning early;
Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
26 Yet they hearkened not unto me, and inclined not their ear; but they hardened their neck; they did worse than their fathers.
Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
27 And if thou speak unto them all these words, and they will not hearken to thee; and if thou call unto them, and they will not answer thee:
“Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
28 Then shalt thou say unto them, This is the nation that hearken not to the voice of the Lord their God, and accept not correction; lost is the truth, and is obliterated from their mouth.
Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
29 Cut off thy flowing hair, and cast it away, and take up on mountain-tops a lamentation; for rejected hath the Lord and forsaken the generation of his wrath.
“‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
30 For the children of Judah have done what is evil in my eyes, saith the Lord: they have set up their abominations in the house which is called by my name, to pollute it.
“‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
31 And they have built the high-places of Thophet, which is in the valley of Ben-hinnom, to burn their sons and their daughters in the fire; which I had not commanded, and which never came into my mind.
Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
32 Therefore, behold days are coming, saith the Lord, that it shall not be called any more Thophet, or The valley of Ben-hinnom, but The valley of slaughter: and they shall bury in Thophet, for want of room.
Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
33 And the carcasses of this people shall become food unto the fowls of the heavens, and unto the beasts of the earth, with none to chase them away.
Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
34 And I will cause to cease from the cities of Judah, and from the streets of Jerusalem, the voice of gladness, and the voice of joy, the voice of the bridegroom, and the voice of the bride; for a desert shall the land become.
Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.