< Jeremiah 46 >

1 The word of the Lord which came to Jeremiah the prophet against the nations:
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Concerning Egypt, against the army of Pharaoh-necho the king of Egypt, which was [posted] by the river Euphrates in Karkemish, which Nebuchadrezzar the king of Babylon smote in the fourth year of Jehoyakim the son of Josiah the king of Judah.
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 Make ye ready shield and buckler, and draw near to the battle.
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Harness the horses, and mount, ye horsemen, and stand forth with helmets: sharpen the spears, and put on the coats of mail.
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 Wherefore have I seen them dismayed, moving backward? while their mighty ones are beaten down, and seek safety in flight, and look not back? There is terror round about, saith the Lord.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 The swift cannot flee away, nor can the mighty man escape: toward the north by the shore of the river Euphrates do they stumble and fall.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 Who is this that cometh up like a stream, whose waters are upheaved like the rivers?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 Egypt cometh up like a stream, and like the rivers are the waters upheaved; and he saith, I will go up, I will cover the land; I will destroy the city and those that dwell therein.
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Come up, ye horses; and rush along wildly, ye chariots; and let the mighty men come forth: Cush and Put, that grasp the shield, and the Ludim, that grasp and bend the bow.
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 And this same day is for the Lord, the Eternal of hosts, a day of vengeance, to be avenged on his adversaries; that the sword may devour, and may be satiated and made drunken with their blood; for there is a sacrifice for the Lord the Eternal of hosts in the north country by the river Euphrates.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Go up into Gil'ad, and fetch balm, O virgin, daughter of Egypt: in vain usest thou many remedies; there is no recovery for thee.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 Nations have heard of thy shame, and thy cry of anguish hath filled the earth; for the mighty man over the mighty have they stumbled, together are both of them fallen.
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 The word which the Lord spoke to Jeremiah the prophet, concerning the coming of Nebuchadrezzar the king of Babylon, to smite the land of Egypt.
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 Announce ye in Egypt, and publish in Migdol, and publish in Noph and in Thachpanches: say ye, Stand fast, and prepare thyself; for the sword devoureth round about thee.
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Why are thy valiant men swept away? not one hath stood, because the Lord did drive him off.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 He caused many to stumble; yea, one also fell over the other; and they said, Arise, and let us return to our own people, and to the land of our birth, from before the wasting sword.
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 They called out there, Pharaoh is king of Egypt, it was but vaunting, he hath let the time appointed pass by.
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 As I live, saith the King, the Lord of hosts is his name, Surely as Thabor is among the mountains, and as Carmel is by the sea, so shall he come.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 Appurtenances of exile make for thyself, O thou inhabitress, daughter of Egypt; for Noph shall be made a waste and be left desolate without an inhabitant.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 O fairest heifer, Egypt! the butcher from the north cometh, he cometh.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Also her hired troops in the midst of her are like fatted calves; for they also are turned round, are fled away together, they do not stand; because the day of their calamity is come upon them, the time of their punishment.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 Her cry shall come like [the hissing of] a serpent; for with an army shall they march, and with axes do they come against her, like hewers of wood.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 They cut down her forest, saith the Lord, though it cannot be searched out; because they are more than the grasshoppers, and there is no number to them.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 Ashamed hath been made the daughter of Egypt: she hath been given up into the hand of the people of the north.
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 The Lord of hosts, the God of Israel, hath said, Behold, I will send visitation on Ahmon of No, and on Pharaoh, and on Egypt, and on her gods, and on her kings; even on Pharaoh, and on those that trust on him;
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 And I will give them up into the hand of those that seek their life, and into the hand of Nebuchadrezzar the king of Babylon, and into the hand of his servants: and afterward shall she be inhabited, as in the days of old, saith the Lord.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 But thou, —fear thou not, O my servant Jacob, and be not dismayed, O Israel; for, behold, I will save thee from afar off, and thy seed from the land of their captivity: and Jacob shall return, and he shall be at rest and at ease, with none to make him afraid.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 Thou, —fear thou not, O Jacob my servant, saith the Lord; for I am with thee: and although I make a full end of all the nations whither I have driven thee, yet of thee will I not make a full end; and I will correct thee in measure; yet wholly will I not leave thee unpunished.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jeremiah 46 >