< Jeremiah 45 >
1 The word which Jeremiah the prophet spoke unto Baruch the son of Neriyah, when he wrote these words in a book out of the mouth of Jeremiah, in the fourth year of Jehoyakim the son of Josiah the king of Judah, saying,
Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
2 Thus hath said the Lord, the God of Israel, concerning thee, O Baruch:
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
3 Thou didst say, Woe is me now! for the Lord hath added grief to my pain; I am wearied in my sighing, and rest have I not found;
Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
4 Thus shalt thou say unto him, Thus hath the Lord said, Behold, what I have built will I pull down, and what I have planted I will pluck up; and so it is with this whole land.
Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
5 And wouldst thou indeed seek great things for thyself? seek them not; for, behold, I will bring evil upon all flesh, saith the Lord; but I will give thy life unto thee as a booty in all the places whither thou mayest go.
Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”