< Jeremiah 39 >

1 In the ninth year of Zedekiah the king of Judah, in the tenth month, that Nebuchadrezzar the king of Babylon came with all his army against Jerusalem, and they besieged it.
A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
2 [And] in the eleventh year of Zedekiah, in the fourth month, on the ninth day of the month, was the city broken in.
A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
3 And then came all the princes of the king of Babylon, and sat down in the middle gate; [namely, ] Neregal-sharezer, Samgar-nebu, Sarsechim, the chief of the eunuchs, Neregal-sharezer, the chief of the magi, with all the residue of the princes of the king of Babylon.
Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
4 And it came to pass when Zedekiah the king of Judah saw them, and all the men of war, that they fled, and went forth out of the city by night, by the way of the king's garden, by the gate between the two walls: and he went out by the way of the plain.
Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
5 But the army of the Chaldeans pursued after them, and they overtook Zedekiah in the plains of Jericho; and they took him, and brought him up to Nebuchadnezzar the king of Babylon to Riblah in the land of Chamath: and he called him to account.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
6 And the king of Babylon slaughtered the sons of Zedekiah in Riblah before his eyes; also all the nobles of Judah did the king of Babylon slaughter.
A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
7 And the eyes of Zedekiah did he blind; and he bound him with brazen fetters, to carry him to Babylon.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
8 And the house of the king, and the houses of the people did the Chaldeans burn with fire, and the walls of Jerusalem did they pull down.
Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
9 And the rest of the people that remained in the city, and those who had run away that had run away to him, with the rest of the people that remained, did Nebuzaradan the captain of the guard carry off into exile to Babylon.
Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
10 But of the poorest of the people, who had nothing, did Nebuzaradan the captain of the guard leave some in the land of Judah, and gave them vineyards and arable fields at the same time.
Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
11 And Nebuchadrezzar the king of Babylon gave charge concerning Jeremiah through means of Nebuzaradan the captain of the guard, saying,
To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
12 Take him, and direct thy eyes to him, and do him not the least harm; but as he may speak unto thee, even so do thou with him.
“Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
13 Then sent Nebuzaradan the captain of the guard, and Nebushazban, the chief of the eunuchs, and Neregal-sharezer, the chief of the magi, and all the chiefs of the king of Babylon, —
Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
14 Even they sent, and took Jeremiah out of the court of the prison, and they committed him unto Gedalyahu the son of Achikam the son of Shaphan, to carry him home: and he remained in the midst of the people.
suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
15 But unto Jeremiah was come the word of the Lord while he was shut up in the court of the prison, saying,
Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
16 Go and say to 'Ebed-melech the Cushi as followeth, Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Behold, I will bring my words [to fulfillment] against this city for evil, and not for good; and they shall be accomplished before thee on that day.
“Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
17 But I will deliver thee on that day, saith the Lord; and thou shalt not be given up into the hand of the men of whom thou hast dread.
Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
18 For I will surely let thee escape, and thou shalt not fall by the sword; but thy life shall be unto thee as a booty; because thou hast put thy trust in me, saith the Lord.
Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”

< Jeremiah 39 >