< Jeremiah 31 >

1 At the same time, saith the Lord, will I be the God for all the families of Israel, and they shall be unto me for a people.
“A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
2 Thus hath said the Lord, The people of those that are escaped of the sword found grace in the wilderness, —even Israel, when it went to find rest.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
3 “From afar is the Lord appeared unto me,” [saying, ] Yea, with an everlasting love have I loved thee; therefore have I guided thee with loving-kindness.
Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
4 Yet again will I build thee up, and thou shalt be built, O virgin of Israel: yet again shalt thou adorn thy timbrels, and go forth in the dances of those that make merry.
Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
5 Yet again shalt thou plant vineyards upon the mountains of Samaria: the planters shall plant, and shall redeem the fruit.
Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
6 For there cometh a day, that the watchers call out upon the mountain of Ephraim, Arise ye, and let us go up to Zion unto the Lord our God.
Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
7 For thus hath said the Lord, Sing for Jacob with joy, and shout at the head of the nations: publish ye, praise ye, and say, The Lord hath helped thy people, the remnant of Israel.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
8 Behold, I will bring them from the north country, and I will gather them from the farthest ends of the earth, among them the blind and the lame, the pregnant woman and she that travaileth with child together: a great assembly shall they return hither.
Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
9 With weeping shall they come, and with supplications will I bring them in: I will lead them by brooks of water in a straight way, whereon they shall not stumble; for I am become a father to Israel, and Ephraim is my first-born.
Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
10 Hear the word of the Lord, O ye nations, and tell it in the isles afar off, and say, He that scattereth Israel will gather him, and keep him, as a shepherd his flock.
“Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
11 For the Lord hath ransomed Jacob, and redeemed him out of the hand of one stronger than he.
Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
12 And they shall come and sing on the height of Zion, and shall come together as a stream to the goodness of the Lord, for wheat, and for wine, and for oil, and for the young of the flocks and of the herds, and their soul shall be as a well-watered garden; and they shall not farther experience grief any more.
Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
13 Then shall the virgin rejoice in the dance, and youth and old men together: and I will change their mourning into gladness, and I will comfort them, and make them rejoice from their sorrow.
’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
14 And I will satiate the soul of the priests with fatness, and my people shall be satisfied with my goodness, saith the Lord.
Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
15 Thus hath said the Lord, A voice is heard in Ramah, groaning, weeping, and bitter lamentation; Rachel is weeping for her children: she refuseth to be comforted for her children because they are not [here].
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
16 Thus hath said the Lord, Refrain thy voice from weeping, and thy eyes from tears; for there is a reward for thy work, saith the Lord, and they shall return from the land of the enemy.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
17 And there is hope for [thee in] thy future, saith the Lord, and thy children shall return to their own borders.
Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
18 I have indeed heard Ephraim bemoaning himself, “Thou hast chastised me, and I was chastised, as an untamed calf; cause me to return, and I will return; for thou art the Lord my God.
“Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
19 Surely after my returning, I repent; and after I am made conscious [by punishment], I smite upon my thigh: I am ashamed, yea, I am confounded, because I bear the disgrace of my youth.”
Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
20 Is not Ephraim a dear son unto me? or a child that I dandle? for whenever I speak of him, I do earnestly remember him again: therefore are my inward parts moved for him; I will surely have mercy upon him, saith the Lord.
Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
21 Set thyself up waymarks, place thyself pillars; direct thy heart toward the highway, the way which thou didst go: return, O virgin of Israel, return to these thy cities.
“Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
22 How long wilt thou roam about, O thou backsliding daughter? for the Lord hath created a new thing on the earth, The woman will go about [seeking for] the husband.
Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
23 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Yet again shall they say this word in the land of Judah and in the cities thereof, when I will bring back again their captivity, —May the Lord bless thee, O habitation of righteousness, O holy mountain.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
24 And there shall dwell therein Judah, and in all his cities together, husbandmen, and they that move about with the flocks.
Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
25 For I have satiated the weary soul, and every grieving soul have I gratified.
Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
26 For this did I awake, and looked about, and my sleep was sweet unto me.
A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
27 Behold, days are coming, saith the Lord, when I will sow the house of Israel and the house of Judah with the seed of man; and with the seed of cattle.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
28 And it shall come to pass, that just as I have watched over them, to pluck up, and to pull down, and to overthrow, and to destroy, and to do harm: so will I watch over them, to build up, and to plant, saith the Lord.
Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
29 In those days shall they not say any more, The fathers have eaten sour grapes, and the children's teeth are set on edge;
“A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
30 But every one shall die for his own iniquity: every man that eateth the sour grapes—his teeth shall be set on edge.
A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
31 Behold, days are coming, saith the Lord, when I will make with the house of Israel, and with the house of Judah, a new covenant;
“Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
32 Not like the covenant that I made with their fathers on the day that I took hold of them by the hand to bring them out of the land of Egypt; which my covenant they have broken, although I was become their husband, saith the Lord;
Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
33 But this is the covenant that I will make with the house of Israel, after those days, saith the Lord, I place my law in their inward parts, and upon their heart will I write it; and I will be unto them for a God, and they shall be unto me for a people.
“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
34 And they shall not teach any more every man his neighbor, and every man his brother, saying, Know the Lord; for they all shall know me, from the least of them even unto their greatest, saith the Lord; for I will forgive their iniquity, and their sin will I not remember any more.
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
35 Thus hath said the Lord, who bestoweth the sun for a light by day, the ordinances of the moon and of the stars for a light by night, who stirreth up the sea that its waves roar—The Lord of hosts is his name:
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
36 If these ordinances ever depart from before me, saith the Lord, then also shall the seed of Israel cease from being a nation before me during all time.
“In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
37 Thus hath said the Lord, If the heavens can be measured above, and the foundations of the earth searched out beneath: then also will I reject all the seed of Israel, for all that they have done, saith the Lord.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
38 Behold, days are coming, saith the Lord, when the city shall be built up to the Lord from the tower of Chananel unto the corner-gate.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
39 And the measuring-line shall yet again go forth opposite it over the hill Gareb, and shall take a turn to Go'ath.
Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
40 And the whole valley of the dead bodies, and of the ashes, and all fields as far as the brook Kidron, unto the corner of the horse-gate toward the east, shall be holy unto the Lord: it shall not be plucked up, nor overthrown any more to eternity.
Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”

< Jeremiah 31 >