< Jeremiah 29 >

1 And these are the words of the letter that Jeremiah the prophet sent from Jerusalem unto the residue of the elders of the exiles, and to the priests, and to the prophets, and to all the people whom Nebuchadnezzar had carried away into exile from Jerusalem to Babylon;
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 (After king Jechonyah and the queen-mother, and the court-officers, the princes of Judah and Jerusalem, and the carpenters, and the locksmiths, were departed from Jerusalem; )
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 By the hand of El'assah the son of Shaphan, and Gemaryah the son of Chilkiyah, [whom Zedekiah the king of Judah sent unto Babylon to Nebuchadnezzar the king of Babylon, ] saying,
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, unto all the exiles, whom I have caused to be carried into exile from Jerusalem unto Babylon,
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Build ye houses, and dwell therein; and plant gardens, and eat their fruit;
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Take ye wives, and beget sons and daughters; and take wives for your sons, and give your daughters to husbands, that they may bear sons and daughters; that ye may multiply there, and not be diminished.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 And seek the welfare of the city whither I have banished you, and pray in its behalf unto the Lord; for in its welfare shall ye fare well.
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 For thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Let not your prophets, that are in the midst of you, and your diviners, deceive you, and do not hearken to your dreams which ye cause to be dreamt;
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 For with falsehood do they prophesy unto you in my name: I have not sent them, saith the Lord.
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 For thus hath said the Lord, Because only after the accomplishment of seventy years for Babylon, will I visit you, and fulfill respecting you my good word, in causing you to return to this place.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 For I alone know the thoughts that I entertain respecting you, saith the Lord, thoughts of peace, and not of evil, to give you a [happy] future and hope.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 And you will call upon me, and ye will go and will pray unto me, and I will hearken unto you.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 And ye will seek me, and shall find me, for ye will search for me with all your heart.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 And I will be found of you, saith the Lord; and I will bring back your captivity, and I will gather you from all the nations, and from all the places whither I have driven you, saith the Lord; and I will cause you to return unto the place whence I have banished you.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Because ye have said, The Lord hath raised us up prophets in Babylon.
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 But thus hath said the Lord concerning the king that sitteth upon the throne of David, and concerning all the people that dwell in this city, your brethren that are not gone forth with you into exile;
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Thus hath said the Lord of hosts, Behold, I will send out against them the sword, the famine, and the pestilence; and I will render them like the detestable figs, that cannot be eaten, from being so bad.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 And I will pursue after them with the sword, with the famine, and with the pestilence, and will make them a horror unto all the kingdoms of the earth, a curse, and an astonishment, and a derision, and a disgrace, among all the nations whither I have driven them;
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 For the reason that they have not hearkened to my words, saith the Lord, since I sent unto them my servants the prophets, causing them to rise up early and sending them; but ye would not hear, saith the Lord.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 But ye—hear ye the word of the Lord, all ye exiles whom I have sent away from Jerusalem to Babylon.
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, concerning Achab the son of Kolayah, and of Zedekiah the son of Ma'asseyah, who prophesy unto you in my name falsehood, Behold, I will give them up into the hand of Nebuchadrezzar the king of Babylon: and he shall smite them before your eyes.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 And a curse shall be derived from them for all the exiles of Judah who are in Babylon, saying, “May the Lord make thee like Zedekiah and like Achab, whom the king of Babylon roasted in the fire;”
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 Because they have done scandalous deeds in Israel, and have committed adultery with the wives of their neighbors, and have spoken in my name falsehood, which I had not commanded them; whereas I am the one that know, and am the witness, saith the Lord.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 And to Shema'yahu the Nechelamite shalt thou say, as followeth,
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, saying, Because thou hast sent in thy name letters unto all the people that are at Jerusalem, and to Zephanyah the son of Ma'asseyah the priest, and to all the priests, saying,
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 The Lord hath appointed thee priest in the place of Jehoyada' the priest, that ye should be superintendents in the house of the Lord, for every man that is mad, and that prophesieth, that thou shouldst put him in the stocks, and in prison:
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 And now, why hast thou not rebuked Jeremiah of 'Anathoth, who prophesieth to you?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 For the reason that he hath sent unto us to Babylon saying, It will last a long time: build ye houses, and dwell therein; and plant gardens, and eat the fruit thereof.
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 And Zephanyah the priest read the letter before the ears of Jeremiah the prophet.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Then came the word of the Lord unto Jeremiah, saying,
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 Send to all the exiles, saying, Thus hath said the Lord concerning Shema'yah the Nechlamite, Whereas Shema'yah hath prophesied unto you, while I have not sent him, and he hath caused you to rely on a falsehood:
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 Therefore thus hath said the Lord, Behold, I will inflict punishment on Shema'yah the Nechlamite, and on his seed; he shall not have a man to dwell in the midst of this people; and he shall not behold the good that I am doing for my people, saith the Lord; because he hath spoken revolt against the Lord.
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremiah 29 >