< Jeremiah 26 >

1 In the beginning of the reign of Jehoyakim the son of Josiah the king of Judah came this word from the Lord, saying,
A farkon sarautar Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo daga wurin Ubangiji,
2 Thus hath said the Lord, Place thyself in the court of the house of the Lord, and speak against all of the cities of Judah, who come to prostrate themselves in the house of the Lord, all the words that I have commanded thee to speak unto them: omit not a word [thereof];
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka tsaya a filin gidan Ubangiji ka kuma yi magana ga dukan mutanen garuruwan Yahuda waɗanda suka zo sujada a gidan Ubangiji. Ka faɗa musu kome da na umarce ka; kada ka bar wata magana.
3 Perhaps it be that they will hearken, and return every man from his evil way, that I may bethink me of the evil, which I purpose to do unto them, because of the wrongfulness of their doings.
Wataƙila su saurara kowanne kuma ya juyo daga mugun hanyarsa. Sa’an nan in yi juyayi in kuma janye masifar da nake shirin kawo a kansu saboda muguntar da suka aikata.
4 And thou shalt say unto them, Thus hath said the Lord, if ye will not hearken unto me, to walk in my law, which I have set before you,
Ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, in ba ku saurare ni, ku kuma bi dokata, wadda na sa a gabanku ba,
5 To hearken unto the words of my servants the prophets, whom I send unto you, yea, making them rise up early, and sending them, while ye have not hearkened:
in kuma ba ku saurari maganganun bayina annabawa, waɗanda na aika muku sau da sau ba (ko da yake ba ku saurara ba),
6 Then will I render this house like Shiloh, and this city will I render a curse unto all the nations of the earth.
to, sai in mai da gidan nan kamar Shilo, birnin nan kuma abin la’ana a cikin al’umman duniya.’”
7 And the priests and the prophets and all the people heard Jeremiah speaking these words in the house of the Lord:
Firistoci, annabawa da dukan mutane suka ji Irmiya yana waɗannan maganganu a gidan Ubangiji.
8 And it came to pass, when Jeremiah had finished speaking all that the Lord had commanded [him] to speak unto all the people, that the priests and the prophets and all the people seized on him, saying, Thou shalt surely die.
Amma da Irmiya ya gama faɗar wa dukan mutanen abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa, sai firistoci, annabawa da dukan mutane suka kama shi suka ce, “Mutuwa za ka yi!
9 Why hast thou prophesied in the name of the Lord, saying, Like Shiloh shall this house be, and this city shall be ruined, [left] without an inhabitant? And all the people assembled themselves against Jeremiah in the house of the Lord.
Me ya sa ka yi annabci da sunan Ubangiji cewa wannan gida zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kango da hamada?” Sai duk mutane suka tattaru kewaye da Irmiya a cikin gidan Ubangiji.
10 But when the princes of Judah heard these things, they came up from the king's house unto the house of the Lord, and sat down at the entrance of the new gate of the Lord's house.
Da fadawan Yahuda suka ji haka, sai suka haura daga fada zuwa gidan Ubangiji suka zazzauna a wuraren zamansu a mashigin Sabuwar Ƙofar gidan Ubangiji.
11 Then said the priests and the prophets unto the princes and unto all the people, as followeth, This man deserveth the punishment of death; for he hath prophesied against this city, as ye have heard with your own ears.
Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
12 Then said Jeremiah unto all the princes and unto all the people, as followeth, The Lord hath sent me to prophesy against this house and against this city all the words that ye have heard.
Sai Irmiya ya ce wa dukan fadawa da kuma dukan mutane, “Ubangiji ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan gida da wannan birni dukan abin da na faɗa.
13 But now amend your ways and your doings, and hearken to the voice of the Lord your God: and the Lord will bethink him of the evil that he hath spoken against you.
Yanzu sai ku gyara hanyoyinku da kuma ayyukanku ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku. Sa’an nan Ubangiji zai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kanku.
14 As for me, behold, I am in your hand: do with me as seemeth good and just in your eyes.
Game da ni dai, ina a hannuwanku; ku yi duk abin da kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku.
15 But know ye for certain, that if ye put me to death, ye will surely place [the guilt of] innocent blood upon yourselves, and upon this city, and upon its inhabitants; for in truth hath the Lord sent me unto you to speak in your ears all these words.
Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
16 Then said the princes and all the people unto the priests and to the prophets, This man is not deserving the punishment of death; for in the name of the Lord our God hath he spoken unto us.
Sai fadawa da dukan mutane suka ce wa firistoci da annabawa. “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.”
17 And then rose up certain men of the elders of the land, and said to all the assembly of the people, as followeth,
Waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka zo gaba suka ce wa dukan taron jama’a,
18 Michah the Morashthite prophesied in the days of Hezekiah the king of Judah. and said to all the people of Judah, as followeth, Thus hath said the Lord of hosts, Zion shall be ploughed up like a field, and Jerusalem shall become heaps of ruins, and the mountain of the house, woody high-places.
“Mika mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya sarkin Yahuda. Ya ce wa dukan mutanen Yahuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “‘Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za tă zama tsibin juji, ƙwanƙolin dutsen haikali kuwa zai zama kurmi.’
19 Did Hezekiah the king of Judah and all Judah attempt to put him to death? behold, he did fear the Lord, and besought the Lord, and the Lord bethought him of the evil which he had spoken against them. And shall we bring a great wickedness on our souls?
“Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
20 And there was also a man that prophesied in the name of the Lord, Uriyah the son of Shema'yahu of Kiryath-ye'arim, who prophesied against this city and against this land in accordance with all the words of Jeremiah;
(To, fa, Uriya ɗan Shemahiya daga Kiriyat Yeyarim wani mutum ne wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji; ya yi annabci irin abu ɗaya gāba da wannan birni da wannan ƙasa yadda Irmiya ya yi.
21 And when king Jehoyakim, with all his mighty men, and all the princes, heard his words, the king sought to put him to death; but when Uriyahu heard it, he was afraid, and fled, and arrived in Egypt;
Da sarki Yehohiyakim da dukan fadawansa da ma’aikatansa suka ji wannan magana, sai sarki ya nemi a kashe shi. Amma Uriya ya ji wannan shiri sai ya gudu zuwa Masar don tsoro.
22 But king Jehoyakim sent some men into Egypt, namely, Elnathan the son of 'Achbor, and some men with him into Egypt:
Sarki Yehohiyakim ya aiki Elnatan ɗan Akbor zuwa Masar, tare da waɗansu mutane.
23 And they fetched Uriyahu out of Egypt, and brought him unto king Jehoyakim, who slew him with the sword, and cast his dead body upon the graves of the common people.
Suka dawo da Uriya daga Masar suka kawo shi wurin Sarki Yehohiyakim, wanda ya kashe shi da takobi aka kuma jefar da gawarsa a makabartar talakawa.)
24 But the hand of Achikam the son of Shaphan was with Jeremiah, so as not to give him up into the hand of the people to put him to death.
Bugu da ƙari, Ahikam ɗan Shafan ya goyi bayan Irmiya, saboda haka ba a ba da shi ga mutane don su kashe shi ba.

< Jeremiah 26 >