< Jeremiah 23 >

1 Woe unto the shepherds that destroy and scatter the flocks of my pasture! saith the Lord.
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 Therefore thus hath said the Lord the God of Israel concerning the shepherds that feed my people, Ye have scattered my flocks, and driven them away, and have not taken care of them: now, behold, I will visit upon you the evil of your doings, saith the Lord.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 And I will indeed gather the remnant of my flock together out of all the countries whither I have driven them; and I will bring them back again to their folds: and they shall be fruitful and multiply.
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 And I will raise up over them shepherds who shall feed them: and they shall fear no more, nor be dismayed, and none of them shall be missing, saith the Lord.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Behold, days are coming, saith the Lord, when I will raise up unto David a righteous sprout, and he shall reign as king, and prosper, and he shall execute justice and righteousness on the earth.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 In his days shall Judah be helped, and Israel shall dwell in safety: and this is his name whereby he shall be called, The Lord is our righteousness.
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 Therefore, behold, days are coming, saith the Lord, when they shall no more say, As the Lord liveth, who hath brought up the children of Israel out of the land of Egypt;
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 But, As the Lord liveth, who hath brought up and who hath led forth the seed of the house of Israel out of the north country, and out of all countries whither I had driven them: and they shall dwell in their own land.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 To the prophets—Broken is my heart within me; all my bones shake; I am like a drunken man, and like a person whom wine hath overcome, because of the Lord, and because of his holy words.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 For of adulterers is the land full; for because of false swearing mourneth the land, dried up are the pastures in the wilderness; because their course was for evil, and their strength was for injustice.
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 For both prophet and priest are hypocrites: yea, in my own house have I found their wickedness, saith the Lord.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 Therefore shall their way be unto them as slippery ways in the darkness; they shall be pushed forward, and fall thereon; for I will bring upon them evil, the year of their punishment, saith the Lord.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 And on the prophets of Samaria have I seen absurdity: they prophesied by Ba'al, and misled my people Israel.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 But on the prophets of Jerusalem have I seen a horrible thing; they commit adultery, and walk in falsehood; and they strengthen the hands of evil-doers, so that not one of these doth return from his wickedness: they are become unto me all of them as Sodom, and its inhabitants as Gomorrah.
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 Therefore thus hath said the Lord of hosts concerning the prophets, Behold, I will feed them with wormwood, and make them drink poison-water; for from the prophets of Jerusalem is hypocrisy gone forth over all the land.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Thus hath said the Lord of hosts, Hearken not unto the words of the prophets that prophesy unto you, they bring you unto vanity: a vision of their own heart do they ever speak, not out of the mouth of the Lord.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 They say indeed unto those that incense me, The Lord hath spoken, Peace shall ye have; and unto every one that walketh in the stubbornness of his own heart, they said, There shall come no evil upon you.
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 For who hath stood in the secret counsel of the Lord, that he could perceive and hear his word? who hath listened to his word and heard it?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 Behold, the storm-wind of the Lord is gone forth in fury, yea, a whirling storm: upon the head of the wicked shall it fall grievously.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 The anger of the Lord will not return, until he have executed, and until he have fulfilled the purposes of his heart: in the end of days shall ye understand this fully.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 I had not sent these prophets, yet they ran: I had not spoken to them, yet they prophesied.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 But if they had stood in my secret counsel, they should have announced my words to my people, and have caused them to turn back from their evil way, and from the wrongfulness of their doings.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 Am I a God for those near at hand, saith the Lord, and not a God for those who are afar off?
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 If a man should hide himself in secret places should I not then see him? saith the Lord. Do I not fill the heavens and the earth? saith the Lord.
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 I have heard what the prophets have said, that prophesy falsely in my name, saying, I have dreamt, I have dreamt.
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 How long shall it be in the heart of the prophets that prophesy falsehood? yea, the prophets of the deceit of their own heart, —
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 [How long] do they think to cause my people to forget my name by their dreams which they relate every man to his neighbor, as their fathers forgot my name for the sake of Ba'al?
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 The prophet that hath had a dream, let him relate his dream; and he that hath received my word, let him speak my word of truth. What hath the straw to do with the corn? saith the Lord.
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 Is not thus my word, like the fire? saith the Lord, and like a hammer that shivereth the rock?
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Therefore, behold, I am against the prophets, saith the Lord, that steal my words every one from his neighbor.
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Behold, I am against the prophets, saith the Lord, that use their own word, and say, [The Lord] saith.
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Behold, I am against those that prophesy with false dreams, saith the Lord, and do relate them, and mislead my people by their falsehoods, and by their vain boasting: while I have not sent them, nor commanded them; and they cannot bring the least profit to this people, saith the Lord.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 And if this people, or the prophet, or a priest, should ask thee, saying, What is the message of the Lord? then shalt thou say unto them, Because of this “What is the message?” will I even cast you off, saith the Lord.
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 And as for the prophet, and the priest, and the people, that will say, “A message of the Lord,” I will even inflict punishment on that man and on his house.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 Thus shall ye say every one to his neighbor, and every one to his brother, What hath the Lord answered? and, What hath the Lord spoken?
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 But “A message of the Lord” shall ye not mention any more; for the message cometh indeed to the man of his [prophetic] word; but ye pervert the words of the living God, of the Lord of hosts our God.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 Thus shalt thou say to the prophet, What hath the Lord answered thee? and, What hath the Lord spoken?
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 But if ye will say, “A message of the Lord,” then thus saith the Lord, Because ye say this word, “A message of the Lord,” and I have sent unto you, saying, Ye shall not say, “A message of the Lord:”
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 Therefore, behold, I am here, and I will tear you completely away, and I will cast you off, and the city that I have given to you and to your fathers, out of my presence;
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 And I will lay upon you an everlasting disgrace, and a perpetual shame, which shall not be forgotten.
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”

< Jeremiah 23 >