< Jeremiah 21 >

1 The word which came unto Jeremiah from the Lord, when king Zedekiah sent unto him Pashchur the son of Malkiyah, and Zephanyah the son of Ma'asseyah the priest, saying,
Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
2 Inquire, I pray thee, in our behalf of the Lord; for Nebuchadrezzar the king of Babylon maketh war against us; peradventure the Lord will deal with us according to all his wondrous deeds, so that he may withdraw from us.
“Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
3 Then said Jeremiah unto them, Thus shall ye say to Zedekiah:
Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
4 Thus hath said the Lord the God of Israel, Behold, I will turn back the weapons of war that are in your hands, wherewith ye fight against the king of Babylon, and against the Chaldeans, who besiege you without the walls, and I will assemble them into the midst of this city.
‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
5 And I myself will fight against you with an outstretched hand and with a strong arm, and in anger, and in fury, and in great wrath.
Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
6 And I will smite the inhabitants of this city, both man and beast: of a great pestilence shall they die.
Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
7 And afterward, saith the Lord, will I give up Zedekiah the king of Judah, and his servants, and the people, and those that are left in this city from the pestilence, from the sword, and from the famine, into the hand of Nebuchadrezzar the king of Babylon, and into the hand of their enemies, and into the hand of those that seek their life: and he shall smite them with the edge of the sword; he will not spare them, nor have pity, nor have mercy.
Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
8 And unto this people shalt thou say, Thus hath said the Lord, Behold, I set before you the way of life, and the way of death.
“Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
9 He that remaineth in this city shall die by the sword, or by the famine, or by the pestilence; but he that goeth out, and runneth away to the Chaldeans that besiege you, shall remain alive, and his life shall be unto him as a booty.
Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
10 For I have set my face against this city for evil, and not for good, saith the Lord: into the hand of the king of Babylon shall it be given up, and he will burn it with fire.
Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
11 And to the house of the king of Judah [say], Hear ye the word of the Lord:
“Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
12 O house of David, thus hath said the Lord, Exercise justice on [every] morning, and deliver him that is robbed out of the hand of the oppressor; lest my fury go forth like fire, and burn so that none can quench it, because of the evil of your doings.
Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
13 Behold, I am against thee, O inhabitress of the valley, [about] the rock of the plain, saith the Lord; who say, Who shall descend down against us? or who shall enter into our habitations?
Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
14 But I will inflict punishment on you according to the fruit of your doings, saith the Lord: and I will kindle a fire in its forest, and it shall devour all its environs.
Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”

< Jeremiah 21 >