< Isaiah 8 >
1 And the Lord said unto me, Take thyself a large table, and write on it with distinct letters, Lemaher-shalal-chash-bas.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 And I was to summon for myself trustworthy witnesses, Uriyah the priest, and Zecharyahu the son of Yeberechyahu.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 And I came near unto the prophetess; and she conceived, and bore a son. Then said the Lord to me, Call his name Maher-shalal-chash-bas.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 For before yet the boy shall know to call, My father, and my mother, the wealth of Damascus and the spoil of Samaria shall be carried away before the king of Assyria.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 And the Lord continued to speak unto me again, saying,
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Forasmuch as this people despiseth the waters of Shiloach that flow softly, and rejoice in Rezin and Remalyahu's son:
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 Yea therefore behold, the Lord bringeth up over them the strong and many waters of the river, —the king of Assyria, and all his glory; and he shall come up over all his channels, and step over all his banks;
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 And he shall penetrate into Judah, overflow and flood over, even to the neck shall he reach; and his outstretched wings shall fill the breadth of thy land, O 'Immanu-el.
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Associate yourselves, O ye people, yet shall ye be broken in pieces; and give ear, all ye of the far portions of the earth: gird yourselves, yet shall ye be broken in pieces; gird yourselves, yet shall ye be broken in pieces.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 Take counsel together, yet shall it come to naught; speak the word, and it shall not stand firm; for with us is God.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 For thus said the Lord to me with the strength of prophecy, and warned me not to walk in the way of this people, saying,
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Call ye not a conspiracy all that this people may call a conspiracy, and what it feareth shall ye not fear, and be not terrified [thereat].
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 The Lord of hosts, him shall ye sanctify; and let him be your fear, and let him be your terror.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 And he will be for a sanctuary; but also for a stone of stumbling and for a rock to fall over unto both the houses of Israel, for a gin and for a snare to the inhabitants of Jerusalem.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 And many shall stumble over them, and fall, and be broken, and snared, and be caught.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Bind up the testimony, seal up the law among my disciples.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 And I will wait for the Lord, that hideth his face from the house of Jacob, and I will hope for him.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Behold, I and the children whom the Lord hath given me are for signs and for tokens in Israel, from the Lord of hosts who dwelleth on mount Zion.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 And when they shall say unto you, “Inquire of those that have familiar spirits, and of the wizards, that whisper, and that mutter:” should not a people inquire of their God? [should we then] in behalf of the living [inquire] of the dead?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 [Hold] to the law and to the testimony: if they are not to speak according to this word, in which there is no light.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 And the [people] shall pass through [the land], hard oppressed and hungry: and it shall come to pass, that when they shall be hungry, they will become enraged, and curse their king and their god, and turn toward on high [for aid].
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 And they will look unto the earth; and behold there are trouble and darkness, dimness of oppression, and they shall be scattered into obscurity.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.