< Isaiah 55 >

1 Ho, every one of ye that thirsteth, come ye to the water, and he too that hath no money: come ye, buy, and eat; yea, come, buy without money and without price wine and milk.
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
2 Wherefore will ye spend money for what is not bread? and your labor for what satisfieth not? hearken then unto me, and eat what is good, and let your soul delight itself in fatness.
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
3 Incline your ear, and come unto me, hear, and your soul shall live; and I will make with you an everlasting covenant, the promised mercies of David, which are sure.
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
4 Behold, for a lawgiver unto the people have I appointed him, a prince and commander to the people.
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
5 Behold, a nation thou knowest not shalt thou call, and a nation that knew thee not shall run unto thee; for the sake of the Lord thy God, and for the Holy One of Israel, for he hath glorified thee.
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
6 Seek ye the Lord, while he may be found, call ye on him, while he is near.
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
7 Let the wicked forsake his way, and the man of unrighteousness his thoughts; and let him return unto the Lord, and he will have mercy upon him, and unto our God, for he will abundantly pardon.
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
8 For not my thoughts are your thoughts, and not your ways are my ways, saith the Lord.
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
9 For as high as the heavens are above the earth, so high are my ways above your ways, and my thoughts above your thoughts.
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
10 For as the rain and the snow come down from heaven, and return not thither, but water the earth, and render it fruitful, and cause it to bring forth plants; and give seed to the sower and bread to him that eateth:
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
11 So shall ever be my word which goeth forth from my mouth, it shall not return unto me without effect; but it accomplisheth what I desire, and it prospereth in that whereto I have sent it.
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
12 For in joy shall ye go out, and in peace shall ye be brought home: the mountains and the hills shall break forth before you into song, and all the trees of the field shall clap their hands.
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
13 Instead of the thorn shall come up the fir-tree, and instead of the nettle shall come up the myrtle; and it shall be unto the Lord for a name, for a sign of everlasting that shall not be cut off.
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< Isaiah 55 >